Skip to main content

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane Da Dama A Filato

Rahotanni sun ce an kashe mutane da dama tare da ƙona gidaje a rikicin da ya ɓarke tsakanin manoma da makiyaya a yankin Mai Tumbi da ke ƙaramar hukumar Mangu a jihar Filato.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Alabo Alfred, ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce tuni da aka tura ‘yan sanda domin tabbatar da zaman lafiya a yankin da rikincin ya shafa
Babban Daraktan Hukumar Tabbatar Da Wanzuwar Zaman Lafiya a Jihar Filato Joseph Lengmang, ya yi Allah wadai da lamarin, inda ya ce sun yi matuƙar baƙin ciki da yadda lamarin ya faru, inda rahotanni masu tayar da hankali suka nuna cewa matsalar tsaro ta tabarbare a yankin, lamarin da ya yi sanadin rasa rayuwa da dukiya mai ɗimbin yawa.

Comments