Skip to main content

An Yiwa Shugaban Najeriya Allurar Rigakafin Cutar Korona

An yi wa shugaban tarayyar Najeriya, Muhammadu Buhari da mataimakinsa, Farfesa Yemi Osinbajo allurar rigakafin cutar Korona (Covid-19) na kamfanin AstraZeneca, kwana daya kacal da soma aikin allurar a duk fadin kasar.

Idan za a tuna, Gwamnatin Tarayya ta sanar a baya cewa lokacin da allurar rigakafin ta iso Nijeriya, Shugaban kasa da jami'an gwamnati da ma dukkan Gwamnonin kasar za su kasance na farko da za a yi wa rigakafin da za nuna a gidan Talabijin na kasa NTA, domin ya zama misali ga sauran 'yan Najeriya da za su biyo baya.

Likitan shugaban kasanr, Dakta Shu’aibu Rafindadi ne ya yiwa shugaban kasar allurar da misalin karfe 11:53 agogon Najeria 10:53 kenan agogon GMT na safiyar yau din nan Asabar, shi ma mataimakin shugaban kasa, Yemi Osinbajo ya bi sahu nan take.

An kuma basu katinan lantarki da ke dauke da bayanan allurar rigakafin su ta hannun Babban Daraktan Hukumar Kula da Lafiya a Matakin Farko (NPHCDA), Dakta Faisal Shuaib.

Najeriya ta samu nasarar karbar allurar ta Oxford a ranar Talata inda ta zama kasa ta uku a Yammacin Afirka da ta karbi allurar bayan Gana da Kwadabuwa.
Cutar Korona dai ta yi mummunan ta'adi ga kasashen duniya, in da Hukumar Lafiya ta Duniya ta bayyana cewa rabo da aga irin hasarar rayuka irin wannan tun Yakin Duniya Na Biyu.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

Gwamnatin Najeriya Ta Shirya Da ASUU

 An kai matsaya tsakanin Kungiyar Malaman Jami'o'i ASUU in da gwamnatin tarayya ta amince da bukatunsu. A jiya jumu'a dai ne suka yi wani zama don ganin malaman sun janye yajin aikin da ya dauki watanni bakwai ana yi. A yanzu dai gwamntin Najeriya ta amince da cire malaman daga tsarin albashi na IPPIS wanda suka jima suna turjiya akai, kuma za ta biya malaman albashin duk watannin da su ke bi. Haka ma ministan kwadagon Najeriya Cris Ngige ya tabbatarwa manema labarai cewa, za a karawa malaman jami'ar alwus da zai kai naira biliyan 35 sabanin yadda yake a da na biliyan 30. Ngige ya kuma ce za a ci gaba da tattaunawa kan sabon tsarin albashi na UTAS muddin an kammala tsara shi. A nasu bangare kungiyar malaman jami'o'in sun yi maraba da wannan yunkuri, in da ake ganin matakin ga alama zai iya kawo karshen dogon yajin aikin da aka dade ana yi.

Me Ku Ka Sani Game Da Labari Maras Daɗi (Negative Story)?

Galibin wasu mutane na ganin 'yan jarida ba su cika bayar da labarai ma su daɗi ba face waɗanda suka shafi tashin hankali da tonon silili da ƙwanƙwanto da kuma na haɗurra. Wannan fahimta kuwa na da nasaba da kasa fahimtar aikin jaridar kansa da wanda ke yin sa. Ni a ganina duk wani labari da ya shafi ayyukan muggan mutane da ya munanawa mutane na gari shi zan mayarwa hankali domin fallasa mai mugunta da farantawa wanda aka zalunta. Bari mu soma da mai sauƙi kafin mu duba ma su sarkakiya. Idan haɗari ya faru, misali na mota ko jirgin sama ko na kasa ko kuma gobara ko ambaliyar ruwa; za mu bayar da labarin. Shin ka san ba muna bayar da labarin ne saboda kawai a ji an mutu ko an kaririye ko an yi hasarar dukiya ba? GA AMSA:  Game da haɗari ko gobara da sauran iftila'i mu kan bayar da wannan labari saboda bayyana halin waɗanda matsalar ta rutsa da su, domin samun agajin hukumomi da masu iya tallafawa. Mu kan bayar da labarin saboda jawo hankalin hukumomin tsaro da saura...