Skip to main content

An Yiwa Shugaban Najeriya Allurar Rigakafin Cutar Korona

An yi wa shugaban tarayyar Najeriya, Muhammadu Buhari da mataimakinsa, Farfesa Yemi Osinbajo allurar rigakafin cutar Korona (Covid-19) na kamfanin AstraZeneca, kwana daya kacal da soma aikin allurar a duk fadin kasar.

Idan za a tuna, Gwamnatin Tarayya ta sanar a baya cewa lokacin da allurar rigakafin ta iso Nijeriya, Shugaban kasa da jami'an gwamnati da ma dukkan Gwamnonin kasar za su kasance na farko da za a yi wa rigakafin da za nuna a gidan Talabijin na kasa NTA, domin ya zama misali ga sauran 'yan Najeriya da za su biyo baya.

Likitan shugaban kasanr, Dakta Shu’aibu Rafindadi ne ya yiwa shugaban kasar allurar da misalin karfe 11:53 agogon Najeria 10:53 kenan agogon GMT na safiyar yau din nan Asabar, shi ma mataimakin shugaban kasa, Yemi Osinbajo ya bi sahu nan take.

An kuma basu katinan lantarki da ke dauke da bayanan allurar rigakafin su ta hannun Babban Daraktan Hukumar Kula da Lafiya a Matakin Farko (NPHCDA), Dakta Faisal Shuaib.

Najeriya ta samu nasarar karbar allurar ta Oxford a ranar Talata inda ta zama kasa ta uku a Yammacin Afirka da ta karbi allurar bayan Gana da Kwadabuwa.
Cutar Korona dai ta yi mummunan ta'adi ga kasashen duniya, in da Hukumar Lafiya ta Duniya ta bayyana cewa rabo da aga irin hasarar rayuka irin wannan tun Yakin Duniya Na Biyu.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

Iran seeks talks with us after threat of attack – Trump

U.S. President Donald Trump has said that Iranian authorities have contacted the United States to seek talks, following his threat to take military action over the killing of protesters in the country. Trump made the statement while speaking to journalists, saying that a meeting between the two sides has already been planned, but that the United States might take some action before the meeting takes place. Meanwhile, a human rights organization in Iran says it has confirmed the deaths of nearly 500 people since the outbreak of the protests. Likewise, some circulating video clips show a site outside Iran where bodies are being kept, with people going there to search for the remains of their relatives who have gone missing.

Sabuwar Kwayar Korona Ta Bulla A Najeriya

A halin yanzu da duniya ke tsakiyar fargaba da rashin sanin makoma, Hukumar Yaki Da Cuta Mai Yaduwa ta NCDC da ke Najeriya, ta fitar da sanarwar barkewar sabon nau'in cutar annobar korona da aka lakabawa suna B.1.1.7. Wannan sabuwar kwayar cutar dai ta fi ta farko saurin yaduwa da matukar hadari wajen kashe mutane, da aka tabbatar da ta kan yadu da kashi 70 cikin dari fiye da na farkon. A watan Disamban 2020 aka samu rahoton bullar sabuwar koronar a kasar Burtaniya da Afirka ta Kudu. Shugaban hukumar NCDC ta kasa Chikwe Ihekweazu ya sanar da hakan a jiya. Ya bayyana cewa hukumar za ta kara azama don yin kandagarkin bazuwar sabon nau'in korona na B.1.1.7 tsakanin jama'a. Wani kwararren likitan Firaministan Burtaniya Boris Johnson mai suna Patrick Vallance, ya bayyana cewa, "daga marasa lafiya 'yan tsakanin shekaru 60 zuwa sama da suka harbu da tsohuwar kwayar cutar a kasar, 10 kan rasa rayukansu a cikin mutum 1000 kowace rana, amma a wannan karon, da wan...

Tinubu Na Gaban Tambuwal A Sokoto

Asiwaju Bola Tinubu, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, ya ba Atiku Abubakar, ɗan takarar jam’iyyar PDP a jihar Sokoto rata a jahar.   Duk da cewa akwai kananan hukumomi 23 a jihar, Tinubu ya tattara mafi yawan kuri’u a kananan hukumomi 10. Alhaji Bola Ahmed Tinubu ya samu kuri’u 101,608, Alhaji Atiku Abubakar ya samu kuri’u 98,080 yayin da Sanata Rabi’u Kwankwaso na jam’iyyar New Nigerian Peoples Party (NNPP) ya zo na uku da kuri’u 314 sannan Peter Obi na jam’iyyar Labour ya samu kuri’u 171. Kananan Hukumomin Da Aka Samu Sakamakonsu TURETA  Waɗanda aka yi ma rajita: 40,746  Waɗanda aka tantance: 16,516  APC 7, 684  LP.  1  NNPP.  9  PDP.  8, 144  KWARE  Waɗanda aka yi ma rajita 74,056  Waɗanda aka tantance 24,776  APC 10,485  LP.  63  NNPP.  11  PDP.  12,242  BODINGA  Waɗanda aka yi ma rajita 86,139  Waɗanda aka tantance 28,054  A 1 ...

Barayi Sun Yiwa Ofishin Jaridar Daily Star Nigeria Kaf

A yau da rana wasu gungun barayi da ba a kai ga ganowa ba sun kai samame ofishin jaridar Daily Star Nigeria da ke jahar Sokoto. Babban editan jaridar, Dr. Mansur Isah Buhari ya tabbatar da wannan lamari, in da ya ce barayin sun yi awon gaba da wasu muhimman kaya da suka hada da kananan kwamfutoci, da akwatin talabijin da ma wasu kudaden da ba a bayyana adadinsu ba kawo yanzu. Dr. Mansur ya ce, "kamar yadda al'adar ofishinmu ta ke, wakilanmu na wajen nemo labarai ni kai na ma na dan fita bana wajen, lokacin da barayin suka auni hakan tare da fasa kofar ofishin in da suka wawushe kome". Jaridar Daily Star Nigeria dai na cikin na gaba gaba daga cikin jerin jaridun yanar gizo da ake da su a Nijeriya yanzu haka.

Wata Mota Cike Da Harsasan Bindiga Ta Fada Rami A Garin Awka Na Jahar Imo

Hankalin jama'a yayi matukar tashi a jiya Lahadi biyo bayan gano wata babbar mota cike da harsasai masu rai a birnin Anacha na jahar Imo da ke kudu maso gabashin tarayyar Najeriya. Rahotannin da suka shigo muna na cewa jami'an tsaron cikin hanzari sun afkawa garin na kasuwanci domin daukar matakin gaggawa kan lamarin.  Babbar motar wadda ke dauke da kwaliyoyin harsasai masu rai ta fada cikin wani rami da ke kan titi, inda dukan harsasan suka zube. Wata majiya da ta tabbatar da faruwar lamarin ta ce: “Motar ta fadi, kuma duk titin na cike da harsasai.  Wasu yaran ma sun debi wasu da hannayensu suka gudu, kafin jami’an tsaro su iso wurin. ”  Majiyar ta ci gaba da bayyana cewa direban babbar motar da mai yi masa hidima sun yi watsi da motar bayan hatsarin ya faru, inda suka yi batan dabo zuwa inda ba a sani ba. Amma wata majiyar ta ce ‘yan sanda sun cafke direban. “Lamarin ya jawo jami'an tsaro masu yawa zuwa yankin hanyar Awka da da safiyar yau. 'Yan sanda sun...

Biden Ya Nemi Magoya Bayansa Su Tsaya A Gida Lokacin Rantsar Da Shi

A daidai lokacin da ake daf da rantsar da sabon shugaban Amurka Joe Biden, an baza dubban jami'an tsaron soji domin murkushe duk wata zanga-zanga da ka iya barkewa. Tun a farkon makon da ya gabata ne dai Hukumar Leken Asiri ta Amurka ta FBI, ta yi gargadin cewa akwai yuwar samun tarzoma a ko'ina a kasar. Zababben shugaban dai ya shawarci jama'a da su yi zaman su a gida ba sai sun halarci bukin rantsarwar ba, ko baya ga matsalar annobar korona akwai yuwar dakarun sojin da aka baza na shirin maganin duk wanda ya nemi daukar dala ba gammo. Shugaba Donald Trump mai barin gado ya bayyana cewa zai bar babban birnin kasar Washington DC tun da sanyin safiyar gobe laraba, don kaucewa yin ido biyu da wanda zai gaje shi. A tarihin kasar dai wannan ne karon farko da za a yi bukin rantsarwa mafi tsaurin tsaro a Amurka, da kuma armashinsa ya ragu, muddin ta tabbata bai samu halarcin jama'a ba.

Biden Ya Doke Trump A Georgia Da Ratar Kuri'u 12,284

 An kammala kirga kuri'un jahar Georgia da ake takaddama kan ta, in da Joe Biden ya lashe jahar da rata mai yawa. Jahar Atlanta Georgia mai yawan kuri'u miliyan biyar da doriya ta zama sha kallo a idon duniya ganin yadda shugaba Donald Trump ya yi zargin shi ne ya samu nasara a jahar kuma ya nemi sai an sake kirga dukan kurin'un da aka kada. A jiya alhamis da yamma ne aka kammala lissafin da ya kwashe kusan fiye da mako daya a na yi, in da ofishin sakataren gwamnatin jahar ya fitar da wannan sanarwa. Ofishin Brad Raffensperger ya bayyana cewa bayan sake kirga dukan kuri'un da hannu, sakamakon da aka samu tun farko yana nan bai sauya ba. Joe Biden ya doke Donald Trump da yawan kuri'u 12,284, yayin da shugaba Donald Trump ya samu 1,872.

'Yan Jarida Na Shan Ɗauri A Rasha

Wata ‘yar jaridar wani gidan talabijin na Rasha, Marina Ovsynnikova, ta fuskanci ɗaurin wata biyu saboda ta bayyana rashin goyon baya akan mamayar da ƙasarta ke ci gaba da yi wa Yukren. Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito cewa, wata kotu ta sanar da kama Ovsynnikova da laifin cin amanar ƙasa, sakamakon ɗaga kwalin da ta yi a kusa da fadar Kremlin mai ɗauke da kalaman da ke cewa, “Putin mai kisan kai ne, yara nawa suka mutu sakamakon aikinka, ka gaggauta dakatar da wannan yaƙi”. Gwamnatin Rasha ta daɗe tana ɗaure masu adawa da mamayar da ta ke yi ma Yukren, tare da bayyana yaƙin  da sunan “aikin dakarun soji na musamman” kuma shugaba Putin ya sha alwashin tsare duk waɗanda aka samu da laifin watsa labarun ƙarya  tsawon shekara goma a gidan jarum.

Thousands of People Are Fleeing Ukraine

Photo: DW Russian troops have entered Ukraine from various directions, including the separatist and Donbas regions from the east, Belarus from the north and Crimea from the south. Residents in Kharkiv, Ukraine's second-largest city, say windows have collapsed as a result of the powerful blasts, as Ukrainian and Russian forces exchange fire. But fighting is also taking place near the capital Kyiv from the north and at ports on the Black Sea coast and in the cities of Odesa and Mariupol from the south. Russia has been carrying out airstrikes on Ukrainian military bases and airports, with fighting intensifying near a key airport near Kyiv. The Ukrainian military claims to have shot down at least six Russian warplanes, while Russia claims to have destroyed more than 70 military bases in Ukraine. Many Ukrainians seek refuge or try to leave the big cities across the country, where thousands of people are fleeing Kyiv.

Kungiyar Boko Haram Ta Saki Bidiyon Yaran Da Aka Sace A Katsina

Kungiyar Boko Haram ta saki wani faifan bidiyo da ke nuna yaran nan daliban makarantar kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina, kwanaki biyar da sace su. A cikin bidiyon an ga wani yaro mai kimanin shekaru sha biyar na magana cikin Hausa: "Don Allah ina rokon gwamnati da kada ta yi amfani da duk wasu 'yan sa kai, a rufe dukan makarantu. Kuma sojojin da ke tafe don taimakonmu don Allah su koma, ba za su iya yi wa (mayakan) kome ba". In ji yaron. A can bayan yaron an ga wasu yara kanana masu yawan gaske da ake umurta da su zauna, kuma da ba su fi shekara goma goma ba, suna kuka tare da rokon a taimaka a cece su daga hannun mayakan. Faifan bidiyon mai tsawon minti daya ya nuna yaran cikin kura da alamar gajiya a tattare da su, sakamakon tafiya mai nisa a kasa. Ana kuma jin muryar daya daga 'yan bindigar na gargadin gwamnati da kada ta dauki kowane matakin amfani da karfi. Yana mai jaddada cewa yaran na cikin koshin lafiya. A ranar jumu'ar da ta gabata ne maharan suka y...