Skip to main content

An Yiwa Shugaban Najeriya Allurar Rigakafin Cutar Korona

An yi wa shugaban tarayyar Najeriya, Muhammadu Buhari da mataimakinsa, Farfesa Yemi Osinbajo allurar rigakafin cutar Korona (Covid-19) na kamfanin AstraZeneca, kwana daya kacal da soma aikin allurar a duk fadin kasar.

Idan za a tuna, Gwamnatin Tarayya ta sanar a baya cewa lokacin da allurar rigakafin ta iso Nijeriya, Shugaban kasa da jami'an gwamnati da ma dukkan Gwamnonin kasar za su kasance na farko da za a yi wa rigakafin da za nuna a gidan Talabijin na kasa NTA, domin ya zama misali ga sauran 'yan Najeriya da za su biyo baya.

Likitan shugaban kasanr, Dakta Shu’aibu Rafindadi ne ya yiwa shugaban kasar allurar da misalin karfe 11:53 agogon Najeria 10:53 kenan agogon GMT na safiyar yau din nan Asabar, shi ma mataimakin shugaban kasa, Yemi Osinbajo ya bi sahu nan take.

An kuma basu katinan lantarki da ke dauke da bayanan allurar rigakafin su ta hannun Babban Daraktan Hukumar Kula da Lafiya a Matakin Farko (NPHCDA), Dakta Faisal Shuaib.

Najeriya ta samu nasarar karbar allurar ta Oxford a ranar Talata inda ta zama kasa ta uku a Yammacin Afirka da ta karbi allurar bayan Gana da Kwadabuwa.
Cutar Korona dai ta yi mummunan ta'adi ga kasashen duniya, in da Hukumar Lafiya ta Duniya ta bayyana cewa rabo da aga irin hasarar rayuka irin wannan tun Yakin Duniya Na Biyu.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

"Ba Ni Goyon Bayan Kowane Dan Takara" - Shugaba Buhari

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bauyana cewa bai zabo kowane dan takara ba, akan haka a bar daliget su zabi wanda 'yan jam'iyya ke so. Bayan ganawa da shugaban kasan jim kadan bayan da shugaban jam'iyyar APC Sanata Abdullahi Adamu ya ayyana Sanata Ahmed Lawan a matsayin dan takarar shugaban kasa na APC, karkashin jagorancin gwamnan jahar Kebbi Atiku Bagudo, sun ce sun tabbatar ma shugaba Buhari cewa har yanzu suna kan bakansu na mika mulki ga kudu. Wannan dai ya nuna daga gobe takara jam'iyyar APC za ta gudanar da zaben fitar da gwani.

Babbar Kotun Tarayya Ta Bayar Da Umurnin Soke Sashe na 84 Da Ya Hana Masu Rike Da Mukaman Siyasa Tsayawa Takara

Babbar Kotun Tarayya da ke zama a Umuahia, Jihar Abia, ta umurci Babban Lauyan Tarayya da ya gaggauta soke sashe na 84 (12) na sabuwar dokar zabe da aka yi wa kwaskwarima.  Yayin da yake rattaba hannu a kan kudirin dokar zabe a watan da ya gabata, shugaba Buhari ya bukaci majalisar dokokin kasar da ta soke sashe na 84 (12), wanda ya haramta wa mambobin majalisar zartaswa tsayawa takara ba tare da yin murabus ba. Shugaban ya kara da cewa, “Sashe na 84 (12) ya kunshi hana masu rike da mukaman siyasa damar kada kuri’a ko zabe a babban taro ko na kowace jam’iyya, domin gabatar da ‘yan takara a kowane zabe.  Sai dai Majalisar Dattawa ta ki yin la’akari da bukatar shugaban kasar, inda ta yi watsi da kudirin dokar da ke neman a yi wa sashen kwaskwarima, inda ‘yan majalisar suka jaddada cewa gyaran sashe na 84 (12) zai saba wa ma’aikatan gwamnati.  

DA DUMI-DUMI 'Yan Majalisar Amurka Sun Soma Zama Don Tsige Trump

'Yan majalisar dokokin Amurka sun soma wani zama na musamman yanzu haka, don shirin tsige shugaba Donald Trump, ana sauran kwanaki 9 kacal a rantsar da zababben shugaban kasar Joe Biden. Kakakin majalisar dattawan kasar Nancy Pelosi a wata hira da tashar talabijin ta NBC, ta ce, "Mista Trump zai fuskanci zahiri ta hanyar girbar abinda ya shuka". Ta ce za su nemi mataimakinsa Mike Pence ya aminta tare da sa hannu akan kudurin dokar da zai nuna amincewa da cewa shugaba Trump bai dace ya shugabanci kasar ba, ko kuma idan har hakan ta ci tura, su soma jefa kuri'ar amincewa da tsige shi a tsakiyar makon nan. Idan har hakan ta tabbata wannan ya nuna Trump ne shugaban Amurka na farko da aka taba tsigewa har sau biyu. Kuma hakan zai bata ma sa suna da makomar siyasa nan gaba. Masana shari'a na ganin bayan tsige shi, zai iya fuskantar tuhuma akan zargin ingiza magoya bayansa su kai hari da zanga-zanga a majalisar dokokin kasar, domin hana amincewa da zaben Joe ...

Jahohin Zamfara, Kaduna Da Jigawa Sun Bada Umurnin Rufe Makarantun Boko

Jahar Jigawa ta bayar da umurnin rufe makarantun Boko daga yau din nan laraba har zuwa wani lokacin da ba a bayyana ba. Jahohi irin su Kaduna, Kano da Sokoto sun bi sahu. Wannan mataki dai a cewar gwamnatin jahar jigawa na da alaka ne da matsalar ci gaba da yaduwar annobar korona. Amma da dama na ganin hakan bai rasa nasaba da harin da 'yan bindiga suka kai a wata makarantar kimiyya ta kwana da ke Kankarar jahar Katsina ranar jumu'ar da ta gabata ne, in da ake jin sun yi awon gaba da dalibai kusan 500. A jiya kungiyar Boko Haram ta fito ta yi ikirarin daukar alhakin sace yaran, abinda ya jefa tsoro da zullumi a zukatan al'umma.

Malami Ya Ce Zai Bi Umurnin Kotu Ya Goge Sashe na 84 (12)

Ministan shari'ar Najeriya Abubakar Malami ya ce cikin gaggawa zai bi umurnin wata babbar kotun Najeriya da ta bukaci a goge sashe na 84 da ya tilasta duk masu rike mukaman siyasa aje mukamansu kwana 30 kafin zabe. KUNA IYA KARANTA: http://tantabaranews.blogspot.com/2022/03/babbar-kotun-tarayya-ta-bayar-da.html Malami dai ya tabbatar da cewa, zai yi ma dokar gyaran fuska. Tun da farko dai shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sanyawa dokar hannu tare da rokon 'yan majalisar dattawan Najeriya da su yi ma ta kwaskwarima wajen cire wannan sashe, amma suka ki amincewa da wannan bukata. Wannan na zuwa ne kwanaki kalilan kafin gudanar da babban zaben jam'iyyar APC da zai gudana a ranar 26 ga wannan wata na Maris. Kuma a na ganin zai iya kara haifar da baraka cikin jam'iyyar.

Halin Da Ake Ciki Kan Yunƙurin Juyin Mulki A Sudan

Jami'an Ɗaukin Gaggawa don Tallafa ma Tsaro a Sudan na Rapid Support Forces (RSF) a yau asabar sun ce sun ƙwace iko da fadar shugaban ƙasa da gidan hafsan hafsoshin soji da babban filin jirgin sauka da tashin jiragen sama a birnin Khartoum a wani yunƙurin juyin mulki da aka yi a lokacin da rikici ya ɓarke tsananinsu da sojoji. Rundunar ta RSF wacce ta zargi sojojin da fara kai mata hari, ta kuma ce sun ƙwace tashoshin jiragen sama a arewacin garin Merowe da kuma El-Obeid a yammacin ƙasar. Rundunar sojin saman Sudan na ci gaba da fatattakar mayaƙan RSF, a cewar wata sanarwa rundunar.   Wasu gidajen talabijin sun nuna wani jirgin soji a sararin samaniyar birnin Khartoum, amma Tantabara News ba ta tabbatar da sahihancin labarin. Rahotanni da ke shigo muna yanzu haka na bayyana cewa ana iya jin ƙarar harbe-harbe a sassa da dama na birnin Khartoum inda wasu shaidun gani da ido da ke bayar da rahoton harbe-harbe a garuruwan da ke makwabtaka da su, lamarin da ya sa ake fa...