Skip to main content

Cire Iyorchia Ayu Daga Shugaban Jam’iyyar PDP Kasada Ce – Debo Ologunagba

A wani zaman sulhu da ake ci gaba da yi a Abuja, gwamnan jahar Rivers Nyesom Wike da tsohon mataimakain jam’iyar PDP na yankin kudu, Chif Olabode George, na cikin sahun gaba wajen ganin jam’iyar ta cire shugabanta na yanzu, Iyochia Ayu daga muƙaminsa muddin a na neman zaman sulhun ya kai ga haifar da ɗa mai ido.

A cewar su, hakan ne kawai zai iya samar da daidaito ga yankin kudancin Najeriya kasancewar ba adalci ne ba ɗan takarar shugaban ƙasa da shugaban jam’iya su fito a yanki guda ba. To, amma kuma wannan buƙata ta gamu da cikas in da a yayin hirarsa da manema labarai a Abuja, Sakataren Jam’iyyar na Ƙasa, Debo Ologunagba, ya ce ba za ta saɓu ba, domin cire shi kasada ce, da za ta iya jefa PDP cikin sabon ruɗani. 
Ya ƙara da cewa, “ai a fili take ƙarara, kamar yadda kundin tsarin jam’iyyar ya tanadar duk lokacin da aka cire shugaban jam’iyya a bisa kowane dalili ne kuwa, to mataimakinsa kan maye gurbinsa kuma ya zama sun fito daga shiya ɗaya. Kazalika, kundin tsarin mulki na  jam’iyyar ya sahale samar da maitaimakan shugaban jam’iyya daga shiyoyin kudu da arewa, kenan idan har aka cire Ayu, shakka babu mataimakinsa Umar Damagun wanda ɗan arewa ne daga jahar Yobe, zai maye gurbinsa”.
Ya ƙara da cewa, dole ne a tafi a haka idan har nasarar jam’iyar ake nema domin kuwa wata shida ne suka rage ga soma manyan zaɓukan ƙasa.

Comments

Popular posts from this blog

Iran seeks talks with us after threat of attack – Trump

U.S. President Donald Trump has said that Iranian authorities have contacted the United States to seek talks, following his threat to take military action over the killing of protesters in the country. Trump made the statement while speaking to journalists, saying that a meeting between the two sides has already been planned, but that the United States might take some action before the meeting takes place. Meanwhile, a human rights organization in Iran says it has confirmed the deaths of nearly 500 people since the outbreak of the protests. Likewise, some circulating video clips show a site outside Iran where bodies are being kept, with people going there to search for the remains of their relatives who have gone missing.

WHEN LIES GO VIRAL: DEFENDING TRUTH IN NIGERIA AND WEST AFRICA’S DIGITAL PUBLIC SPHERES

Across Nigeria and West Africa, digital technology has reshaped how citizens engage with information, governance, and public debate. Mobile phones and social media platforms have become dominant sources of news, especially for young people and communities with limited access to traditional media. While this transformation has expanded civic participation and freedom of expression, it has also intensified the spread of misinformation, posing serious risks to democracy, public health, and social cohesion. Misinformation is no longer a marginal problem. It is a structural challenge that affects elections, security, development communication, and trust in public institutions. Addressing it requires coordinated action that combines ethical journalism, media literacy, platform accountability, and evidence based policy responses. THE DIGITAL INFORMATION LANDSCAPE IN NIGERIA AND WEST AFRICA Nigeria is Africa’s most populous country and one of its most digitally active societies. So...

Murtala Abdulkadir Dan Iya Gambun Sakkwatawa

Alhaji Murtala Abdulkadir Dan Iya ya shahara wajen ayyukan jinƙai a Jihar Sokoto tsawon  shekarun ya zuwa yanzu. Alhaji Murtala Abdulkadir Dan Iya shugaban Hukumar Bayar Da Tallafin Ƙaro Karatu ta Jihar Sokoto  A tattaunawar da jaridar Tantabara News ta yi da Nura Muhammad Chiso, wanda ke jagorancin daya daga cikin ƙungiyoyin Alhaji Murtala Abdulkadir Dan Iya, mai suna da ke bayar da tallafi da wayar da kan al'umma a jihar ta Sokoto, ya bayyana tarin manyan tallafan da wannan shahararren ɗan kasuwa, kuma ɗan siyasa ya yi wa dubban mutane mabukata a jihar, lamarin da ya ƙara ɗaukaka darajar sunansa a cikin jihar da ma wajenta. N ura Muhammad Chiso  Nura Muhammad Chiso ya ce, "wannan aikin alheri na shugaban Hukumar Bayar Da Tallafin Ƙaro Karatu ta Jihar Sokoto, wani babban aikin alheri ne da ya gane dubban jama'a talakawa har hakan ya sa suke kiran sa da gambun Sakkwatawa saboda faranta musu rai da yake yi". Ga wa...