Skip to main content

Shugaban Gwamnatin Jamus Frank-Walter Steinmeier Na Shan Suka

Jami'an Ukraine da na Poland sun soki shugaban Jamus Frank-Walter Steinmeier da cewa yana dasawa da  Rasha. Jakadan Ukraine a birnin Berlin ya kaurace wa wani bikin zaman lafiya da mawakan Rasha da Steinmeier ya shirya.
Gidan rediyon DW ya ruwaito cewa, Jakadan Ukraine a Jamus Andriy Melnyk da mataimakin firaministan Poland Jaroslaw Kaczynski  sun caccaki shugaban Jamus Frank-Walter Steinmeier sakamakon alakar da aka lura yana da ita da kasar Rasha.
Melnyk ya gaya wa jaridar Tagesspiegel cewa, "Steinmeier na da abin da ya ke boyewa dangane da wannan alaka tasa da Rasha".
Ya kara da cewa, "mutanen da ke da alaka da Steinmeier kamar Jens Plötner, mai ba wa Wazirin Jamus, Olaf Scholz shawara kan manufofin kasashen waje, da Sakatariyar Ma'aikatar Harkokin Wajen Jamus Andreas Michaelis hadi da karin wasu, na daga cikin wadanda ake zargin cewa ba za su rasa hannu ga wannan kusanci ba".
Kaczynski ya kuma bayyana cewa manufofin ketare na Jamus na da tasgaro in da bai gamsu da yadda ake tafiyar da su ba, a maimakon haka, ya yi kira da a kara yawan sojojin Amurka da ke nahiyar Turai da kashi 50 cikin 100 domin tunkarar matsalar tsaro da ke kunno kai a nahiyar.
Wannan furuci na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatin Jamus ke neman sauya salon siyasarta dangane da kasar Rasha, sakamakon mamayar da aka yi wa Ukraine.
Shugaban gwamnatin Jamus Olaf Scholz ya ƙara kashe kuɗin tsaron Jamus kimanin Euro biliyan 100 wanda wannan ya karya daɗaɗɗen abin da ya faru bayan yakin cacar baka don ba da agaji ga Ukraine.

Koda ya ke kasar Jamus din a hannu daya, ta yi abin a zo a gani in da ta yi maraba da kusan 'yan gudun hijirar Ukraine 300,000.

Melnyk ya ci gaba da cewa, "Wani abin takaici ma shi ne, Steinmeier ya taba samar da tashar yanar gizo ta musamman domin samar da ingantacciyar hanyar sadarwa tsakanin Jamus da Rasha shekaru da yawa", Ya kara da cewa, "a wurin Steinmeier, dangantakar kasarsa da Rasha ta kasance gagaruma mai mahimmanci - har ma da tsarki, duk kuwa da abinda ya faru, hatta mamayar da Rasha ta yi ma Ukraine babu wata alamar zai taka rawar a zo a gani ko ma ya yi tir da matakin."

Jakadan Ukraine a Berlin a baya ya fito fili ya soki Steinmeier ta hanyar kin gayyatar da aka yi masa zuwa wani bikin zaman lafiya da ya shirya tare da mawakan Rasha.

"A nawa ra'ayi, wasan kwaikwayon ya kasance wata alama ce mai yi wa Moscow dadi, watakila ma don tallata manufofin Putin," in ji Melnyk.

 Melnyk ya lura cewa gwamnatin Jamus ba ta fito ba game da raba shirye-shiryenta na isar da makamai.  Jakadan ya lura cewa ya karanta labarin cewa Jamus na shirin baiwa Ukraine makamai da kudinsu ya kai Euro miliyan 308, to sai dai babu wani abu zahiri da ya nuna hakan.

Shi kuma mataimakin firaministan kasar Poland Kaczynski ya ce, "Turai na bukatar karin sojojin Amurka saboda karuwar ta'addancin Rasha," ya kara da cewa Jamus na jan kafa ga Moscow."
newsweek.com
Sannan a cewar sa ya zama wajibi ga shugaba Olaf Scholz ya taka rawar a zo a gani domin samar da 'yanci ga kasashen turai".

Haka ma Kaczynski ya ce kasar Poland shirye ta ke ta tura makaman nukiliyar Amurka a yankinta, ko da yake ba a yi wata tattaunawa da Washington kan lamarin ba.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

NDE Commences Sustainable Training and Loan Disbursement To 100 Youths in Sokoto

The National Directorate of Employment (NDE) has commenced Sustainable Agricultural Development Scheme (SADTS) and loand disbursement to 100 youths in Sokoto. Director-General of NDE, Malam Abubakar Fikpo, disclosed this on Tuesday in Sokoto during the orientation of agricultural loans disbursement held at Shamsuddeen Plaza. Fikpo represented by the Sokoto State NDE Coordinator Mrs Eunice J. Danmallam, said beneficiaries are entitled to N100,000 each at 9 per cent interest rate. He said the beneficiaries were captured under the Agricultural Enhancement Scheme (AES) and Community-Based Agricultural Empowerment Scheme (CBAES). He added they were also under Graduate Agricultural Empowerment Scheme (GAES) and Sustainable Agricultural Development and Empowerment Scheme (SADES). Fikpo said that six months moratorium was given after which  beneficiaries were expected to repay the loan in installments over a period of three years. Dan Mallam expressed gr...

The Nigerian Governors Forum Describe The Militant Attack On Benue State Governor As Shocking

The Nigerian Governors Forum (NGF) has described the militant attack on the Benue State governor as "shocking" and "scary".  Governor Samuel Ortom's delegation was attacked by gunmen on Saturday on the Makurdi-Gboko road, when he visited his farm.  In a statement issued by the group's chairman and Ekiti State Governor Kayode Fayemi on Sunday, the NGF congratulated Ortom for the escape from the attack which it said was "scary and offensive".  Inspector General of Police Mohammed Adamu also condemned the attack and ordered that security be beefed up on the governor and an investigation launched.  "The NGF has said in a loud voice that efforts to rehabilitate Benue State will not succeed," the statement said.  "One of the relatives of a former governor of the state was recently killed. This kind of act of violence must be stopped for whatever reason to kill the people of Benue."