Skip to main content

Shugaban Gwamnatin Jamus Frank-Walter Steinmeier Na Shan Suka

Jami'an Ukraine da na Poland sun soki shugaban Jamus Frank-Walter Steinmeier da cewa yana dasawa da  Rasha. Jakadan Ukraine a birnin Berlin ya kaurace wa wani bikin zaman lafiya da mawakan Rasha da Steinmeier ya shirya.
Gidan rediyon DW ya ruwaito cewa, Jakadan Ukraine a Jamus Andriy Melnyk da mataimakin firaministan Poland Jaroslaw Kaczynski  sun caccaki shugaban Jamus Frank-Walter Steinmeier sakamakon alakar da aka lura yana da ita da kasar Rasha.
Melnyk ya gaya wa jaridar Tagesspiegel cewa, "Steinmeier na da abin da ya ke boyewa dangane da wannan alaka tasa da Rasha".
Ya kara da cewa, "mutanen da ke da alaka da Steinmeier kamar Jens Plötner, mai ba wa Wazirin Jamus, Olaf Scholz shawara kan manufofin kasashen waje, da Sakatariyar Ma'aikatar Harkokin Wajen Jamus Andreas Michaelis hadi da karin wasu, na daga cikin wadanda ake zargin cewa ba za su rasa hannu ga wannan kusanci ba".
Kaczynski ya kuma bayyana cewa manufofin ketare na Jamus na da tasgaro in da bai gamsu da yadda ake tafiyar da su ba, a maimakon haka, ya yi kira da a kara yawan sojojin Amurka da ke nahiyar Turai da kashi 50 cikin 100 domin tunkarar matsalar tsaro da ke kunno kai a nahiyar.
Wannan furuci na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatin Jamus ke neman sauya salon siyasarta dangane da kasar Rasha, sakamakon mamayar da aka yi wa Ukraine.
Shugaban gwamnatin Jamus Olaf Scholz ya ƙara kashe kuɗin tsaron Jamus kimanin Euro biliyan 100 wanda wannan ya karya daɗaɗɗen abin da ya faru bayan yakin cacar baka don ba da agaji ga Ukraine.

Koda ya ke kasar Jamus din a hannu daya, ta yi abin a zo a gani in da ta yi maraba da kusan 'yan gudun hijirar Ukraine 300,000.

Melnyk ya ci gaba da cewa, "Wani abin takaici ma shi ne, Steinmeier ya taba samar da tashar yanar gizo ta musamman domin samar da ingantacciyar hanyar sadarwa tsakanin Jamus da Rasha shekaru da yawa", Ya kara da cewa, "a wurin Steinmeier, dangantakar kasarsa da Rasha ta kasance gagaruma mai mahimmanci - har ma da tsarki, duk kuwa da abinda ya faru, hatta mamayar da Rasha ta yi ma Ukraine babu wata alamar zai taka rawar a zo a gani ko ma ya yi tir da matakin."

Jakadan Ukraine a Berlin a baya ya fito fili ya soki Steinmeier ta hanyar kin gayyatar da aka yi masa zuwa wani bikin zaman lafiya da ya shirya tare da mawakan Rasha.

"A nawa ra'ayi, wasan kwaikwayon ya kasance wata alama ce mai yi wa Moscow dadi, watakila ma don tallata manufofin Putin," in ji Melnyk.

 Melnyk ya lura cewa gwamnatin Jamus ba ta fito ba game da raba shirye-shiryenta na isar da makamai.  Jakadan ya lura cewa ya karanta labarin cewa Jamus na shirin baiwa Ukraine makamai da kudinsu ya kai Euro miliyan 308, to sai dai babu wani abu zahiri da ya nuna hakan.

Shi kuma mataimakin firaministan kasar Poland Kaczynski ya ce, "Turai na bukatar karin sojojin Amurka saboda karuwar ta'addancin Rasha," ya kara da cewa Jamus na jan kafa ga Moscow."
newsweek.com
Sannan a cewar sa ya zama wajibi ga shugaba Olaf Scholz ya taka rawar a zo a gani domin samar da 'yanci ga kasashen turai".

Haka ma Kaczynski ya ce kasar Poland shirye ta ke ta tura makaman nukiliyar Amurka a yankinta, ko da yake ba a yi wata tattaunawa da Washington kan lamarin ba.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Da Dumi Dumi An Ceto Yaran Da Aka Sace A Katsina

Sakataren gwamnatin jahar Katsina Alhaji Mustapha Inuwa ya fitar da sanarwar cewa an samu nasarar ceto daliban nan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su daga makarantar kwanan ta Kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina. Ya ce an ceto yaran su 340, kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta isowa jahar daga Tsafen jahar Zamfara. Ana sa ran gobe jumu'a za su gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kafin daga bisani a sada su da iyayensu. Sauran bayani zai zo nan gaba.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey