Skip to main content

Shugaban Gwamnatin Jamus Frank-Walter Steinmeier Na Shan Suka

Jami'an Ukraine da na Poland sun soki shugaban Jamus Frank-Walter Steinmeier da cewa yana dasawa da  Rasha. Jakadan Ukraine a birnin Berlin ya kaurace wa wani bikin zaman lafiya da mawakan Rasha da Steinmeier ya shirya.
Gidan rediyon DW ya ruwaito cewa, Jakadan Ukraine a Jamus Andriy Melnyk da mataimakin firaministan Poland Jaroslaw Kaczynski  sun caccaki shugaban Jamus Frank-Walter Steinmeier sakamakon alakar da aka lura yana da ita da kasar Rasha.
Melnyk ya gaya wa jaridar Tagesspiegel cewa, "Steinmeier na da abin da ya ke boyewa dangane da wannan alaka tasa da Rasha".
Ya kara da cewa, "mutanen da ke da alaka da Steinmeier kamar Jens Plötner, mai ba wa Wazirin Jamus, Olaf Scholz shawara kan manufofin kasashen waje, da Sakatariyar Ma'aikatar Harkokin Wajen Jamus Andreas Michaelis hadi da karin wasu, na daga cikin wadanda ake zargin cewa ba za su rasa hannu ga wannan kusanci ba".
Kaczynski ya kuma bayyana cewa manufofin ketare na Jamus na da tasgaro in da bai gamsu da yadda ake tafiyar da su ba, a maimakon haka, ya yi kira da a kara yawan sojojin Amurka da ke nahiyar Turai da kashi 50 cikin 100 domin tunkarar matsalar tsaro da ke kunno kai a nahiyar.
Wannan furuci na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatin Jamus ke neman sauya salon siyasarta dangane da kasar Rasha, sakamakon mamayar da aka yi wa Ukraine.
Shugaban gwamnatin Jamus Olaf Scholz ya ƙara kashe kuɗin tsaron Jamus kimanin Euro biliyan 100 wanda wannan ya karya daɗaɗɗen abin da ya faru bayan yakin cacar baka don ba da agaji ga Ukraine.

Koda ya ke kasar Jamus din a hannu daya, ta yi abin a zo a gani in da ta yi maraba da kusan 'yan gudun hijirar Ukraine 300,000.

Melnyk ya ci gaba da cewa, "Wani abin takaici ma shi ne, Steinmeier ya taba samar da tashar yanar gizo ta musamman domin samar da ingantacciyar hanyar sadarwa tsakanin Jamus da Rasha shekaru da yawa", Ya kara da cewa, "a wurin Steinmeier, dangantakar kasarsa da Rasha ta kasance gagaruma mai mahimmanci - har ma da tsarki, duk kuwa da abinda ya faru, hatta mamayar da Rasha ta yi ma Ukraine babu wata alamar zai taka rawar a zo a gani ko ma ya yi tir da matakin."

Jakadan Ukraine a Berlin a baya ya fito fili ya soki Steinmeier ta hanyar kin gayyatar da aka yi masa zuwa wani bikin zaman lafiya da ya shirya tare da mawakan Rasha.

"A nawa ra'ayi, wasan kwaikwayon ya kasance wata alama ce mai yi wa Moscow dadi, watakila ma don tallata manufofin Putin," in ji Melnyk.

 Melnyk ya lura cewa gwamnatin Jamus ba ta fito ba game da raba shirye-shiryenta na isar da makamai.  Jakadan ya lura cewa ya karanta labarin cewa Jamus na shirin baiwa Ukraine makamai da kudinsu ya kai Euro miliyan 308, to sai dai babu wani abu zahiri da ya nuna hakan.

Shi kuma mataimakin firaministan kasar Poland Kaczynski ya ce, "Turai na bukatar karin sojojin Amurka saboda karuwar ta'addancin Rasha," ya kara da cewa Jamus na jan kafa ga Moscow."
newsweek.com
Sannan a cewar sa ya zama wajibi ga shugaba Olaf Scholz ya taka rawar a zo a gani domin samar da 'yanci ga kasashen turai".

Haka ma Kaczynski ya ce kasar Poland shirye ta ke ta tura makaman nukiliyar Amurka a yankinta, ko da yake ba a yi wata tattaunawa da Washington kan lamarin ba.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

Breaking: Chadian President Idris Deby Is Dead

  Chadian President Idris Deby died while leading the country's security forces over the weekend, fighting rebels on the northern country's border with Libya.  President Deby is widely expected to win the country's general election by 80 percent after seeking a sixth term.  The military has dissolved parliament and announced that it would hold power for 18 months before new elections.  Idris Deby took power in Chad in 1990 after overthrowing the government of former President Hissene Habry, and has ruled Chad for 30 years.

Stepping Down Not The Right Option - Osinbajo

Vice president Yemi Osinbajo has denied reports that he intends to step down for a certain presidential aspirant ahead of the presidential primary of the All Progressives Congress (APC). The denial is contained in a statement by the chairman of Osinbajo’s campaign council, Richard Akinnola on Sunday. According to the statement, the people behind the speculation are “afraid of the huge political support base of the Vice President, Prof. Yemi Osinbajo,” adding that the VP is ready for the presidential primary scheduled to hold between June 6 and 8. The campaign council “welcomes our distinguished delegates from across the country to Abuja for our presidential primaries. “As you settle down in Abuja, we implore you to kindly disregard various fake news making the rounds that Prof. Yemi Osinbajo has stepped down. “Osinbajo would be hoping to clinch the ticket of the ruling party with much desire to take over from his principal, President Muhammadu Buhari at the end of his tenur...

'Yan Bindiga Sun Kai Hari Gidajen Ma'aikatan Filayen Jiragen Saman Najeria Tare Da Sace Mutum 11

Rahotanni sun ce wasu ‘yan bindiga sun kai hari a gidajen ma'aikatan Hukumar Filin Jirgin Saman Tarayyar Najeriya da ke Kaduna, inda suka yi awon gaba da akalla mutane 11. Rahotannin baya-bayan nan sun kuma bayyana cewa ‘yan bindigar sun yi nasarar sace ma’aikacin Hukumar Kula da Sararin Samaniyar Najeriya (NAMA)A, da matarsa, da jami’in Hukumar Kula da Yanayi ta Kasa (NIMET) da ya’yansa, kuma har yanzu ba a san inda suke ba. Satar mutane ya zama ruwan dare a Najeriya a yau, kuma kusan kowace safiya ana samun rahotannin kashe-kashe ko satar mutane don neman kudin fansa.  A makon da ya gabata ne shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya sha alwashin kawo karshen satar mutane a Najeriya amma ga dukkan alamu kalaman nasa ba su yi tasiri ba. 

PDP Na Shirin Korar Wike

Gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya shigar da Æ™ara domin hana wani sabon yunÆ™urin jam’iyyar PDP dakatar da shi daga cikinta, kuma ya buÆ™aci kotun da ta É—auki mataki ga duk masu wannan aniya.  ÆŠaya daga cikin jigajigan jam'iyyar PDP da suka mayar da martani kan Æ™arar da gwamna Wike ya shigar, Mahdi Shehu, ya mayar da martani a ranar Litinin da ta gabata inda ya wallafa a shafinsa na twitter wata sanarwa cewa, “Wike ya shigar da Æ™ara kan jam’iyyar PDP mai lamba FHC/ABJ/CS/139/2023 ta hannun lauyoyinsa, DY Musa (SAN);  Douglas Moru, da C. C. Chibuike, yana neman a ba shi umarnin hana a kore shi daga PDP.”   Wike dai ya yi ta famar ruguza jam’iyyar har ma ya rasa inda za shi. Gwamnan na Ribas ya zamewa jam'iyyar PDP Æ™adangaren bakin tulu, irin yadda ya ke uwa da makarbiya tun bayan da dangantaka ta soma tsami tsakaninsa da wasu jigajigan jam'iyyar ciki kuwa har da gwamnan jahar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal.  

Farkawar Matan Afirka

Afirka nahiya ce mai dogon tarihi. Tun asali,  yawancin Turawa sun yi kokarin sanya idanu a kan nahiyar, sun ziyarce ta don neman ko dai kasuwanci, wanda a wancan lokacin wani nau'i ne na cinikin bayi ko kuma daga baya ya koma ga cinikin kayan masarufi kamar su gyada, auduga, fatun dabbobi da makamantansu. Zuwan Larabawa kuma, a wasu lardunan Afirka na lokacin, gami da yankin da ake kira "Sudaniyya", wanda ya hada da Sudan, Najeriya, Chadi, da wasu sassan Jamhuriyar Nijar, ya haifar da yaduwar Musulunci da al'adun Gabas. Daga baya, zuwan Bature ya kawo kiristanci, ilimin yamma da sauran manufofin Turawa. Nahiyar Afirka sannu a hankali tana juyawa zuwa matakai daban-daban; daga duhun kai har zuwa halin da ake ciki a yau. Ilimin addini da na zamani sun samu gindin zama a kasashen Afirka, amma har yanzu mata suna baya a wannan tafiyar. Sau da yawa za ka ga mata a yankunan karkara har ma da wasu biranen Afirka ci...

Filin Jiragen Sama Na Malam Aminu Kano Zai Ci Naira Biliyan 700

Ministan suhurin jiragen sama Alhaji Hadi Sirika, ya bayyana cewa majalisar zartaswata Æ™asa ta amince da ware fiye da naira biliyan É—ari bakwai domin aikin kwangilar gyaran filin sauka da tashin jiragen na sama na duniya na Malam Aminu Kano, wanda ya ce za kammala a cikin shekara É—aya rak. Majalisar zartaswa ta Æ™asa ta kuma amince da ware naira biliyan É—ari da goma sha bakwai domin gudanar da kwangilar gina cibiyar bincike akan man fetur ta Oloibir a yankin Naija Delta. Ministan Æ™asa a ma’aikatar albarkatun man fetur, Timipre Sylva ne ya shaidawa ‘yan jaridar fadar shugaban Æ™asa hakan, inda ya ce za a kammala aikin kwangilar a cikin shekaru biyu da rabi. Ya ce tun a 1980 gwamnatin Alhaji Shehu Aliyu Shagari ta soma aikin, amma daga bisani aka yi watsi da shi wanda a yanzu zai zama É—aya daga cikin manyan ayyukan da za a ci ga da tunawa da shugaba Muhammadu Buhari a yankin Naija Delta mai arzikin man fetur.

Dalar Amurka Na Fuskantar Barazanar Durkushewa

Shugaban kasar Brazil Luiz Inacio Lula da Silva ya soki kasar Amurka akan irin rawar da dala ke takawa a tattalin arzikin duniya tare da yin kakkausar suka ga asusun lamuni na duniya na IMF. Lula ya yi waÉ—annan kalamai a wata ziyarar aiki da ya kai Chana, jiya Alhamis a birnin Shanghai a wani bikin kaddamar da takwaransa, Dilma Rousseff a matsayin sabuwar shugabar bankin raya kasashen BRICS, da gamayyar kasashenn Brazil da Rasha da Indiya da Chana da kuma Afirka ta Kudu suka samar. "Me ya sa kowace Æ™asa za a danganta da dala don kasuwanci? Wanene ya yanke shawarar dala za ta zama kuÉ—in duniya?"  Ya Æ™ara da cewa me yasa banki kamar bankin BRICS ba zai iya samun kuÉ—in da zai gudanar da hulÉ—ar kasuwanci tsakanin Brazil da Chana ba, da ma sauran Æ™asashen duniya? Ya ce yana mamakin yadda Æ™asashe cike da rauni  su ke bin sawun amfani da dala wajen gudanar da kasuwanci alhali suna iya hakan da kuÉ—aÉ—ensu. A wata ganawa tsakanin sa da shugaban Chana Xi Jinping, da kuma ya ...

Nigerian President Vaccinated Against Covid-19

Nigerian President Muhammadu Buhari and his vice president, Professor Yemi Osinbajo, have been vaccinated with AstraZeneca vaccine, just one day after the nationwide vaccination campaign. Earlier, the Federal Government announced that as soon as the vaccine arrives in Nigeria, the President, government officials and all Governors will be at the forefront of the immunization drive which would be shown on the National Television (NTA) to set an example for other Nigerians, as well as allay their fears about the legitimacy of the vaccine. The president's doctor, Dr. Shuaibu Rafindadi, vaccinated the president at 11:53 a.m. Nigerian time (10:53 a.m. GMT) on Saturday, and Vice President Yemi Osinbajo immediately joined the process. They were also provided with electronic immunization cards by the Director General of Primary Health Care Development (NPHCDA), Dr. Faisal Shuaib. Nigeria successfully started the vaccination on Tuesday, becoming the third West African country to ...

National Directorate of Employment (NDE) Disburses 100,000 as a Loan to 108 Agricultural Empowerment Scheme Beneficiaries in Sokoto

The state Coordinator of the agency said this was to enable the beneficiaries to be self reliant and contribute their quota to the development of the country. She said the programme was a combined orientation made up of 108 beneficiaries of Agricultural Empowerment Scheme, Community Based Agricultural Empowerment Scheme, Sustainable Agricultural Development Empowerment Scheme and Graduate Agricultural Empowerment Scheme that were given loans of N100, 000 each. Mrs. Danmallam added that the beneficiaries are graduates of NDE agricultural Extension, Poultry and Vegetable production. She said the money disbursed to them was a loan facility which would attract a single digit simple interest rate of 9 % and will have a moratorium of six months before beneficiaries will start paying back and it is repayable in three years.  Therefore, urged the them to ensure timely repayment to enable other unemployed persons to also benefit. In his goodwill message, ...

Israel Targets Journalists

GAZA: An Israeli airstrike destroyed a high-rise building in Gaza City that housed offices of The Associated Press and other media outlets on Saturday, the latest step by the military to silence reporting from the territory amid its battle with the militant group Hamas. The strike came nearly an hour after the military ordered people to evacuate the building, which also housed Al-Jazeera, other offices and residential apartments. The strike brought the entire 12-story building down, collapsing with a gigantic cloud of dust. There was no immediate explanation for why it was attacked. The strike came hours after another Israeli air raid on a densely populated refugee camp in Gaza City killed at least 10 Palestinians from an extended family, mostly children, in the deadliest single strike of the current conflict. Both sides pressed for an advantage as cease-fire efforts gathered strength. The latest outburst of violence began in Jerusalem and has spread across the region, with...