Skip to main content

Shugaban Rasha Ya Nunawa Biden Yatsa

ewn.co.za
Shugaban kasar Rasha Vladimir Putin ya ce kalaman da shugaban Amurka Joe Biden ya yi ba za su tafi a banza ba. Yana dai mayar da martani ne akan kalaman shugaba Amurka da ya ce, "Putin azzalumi ne kuma wanda ya aikata manyan laifukan yaki".

Sai dai shugaba Putin ya ce ba za ta taba yuwa Rasha ta yafe ma Amurka ta kowane fanni ba sakamakon wadannan kalamai da ya kira, "na cin zarafin kasarsa".
Yanzu haka dai yakin da kasashen Ukraine da Rasha ke ci gaba da gwabzawa ya shiga mako na uku in da munana hare-haren da dakarun Rasha ke kaiwa suka yi sanadiyyar hallakar fararen hula da dama, ciki kuwa har da yara kanana.
npr.org
Kasashen da ke karkashin kungiyar tsaro ta NATO sun zakuda gefe guda ba tare da amincewa su tsunduma cikin yakin ba, in da suka bayar da hujjar cewa tsunduma yakin na iya haifar da yakin duniya na uku. Sai dai a maimakon haka sun tsananta sakawa Rasha karin takunkumai da suka hada da kin sayen man da ta ke hakowa, da rufe asusun ajiyar manyan jami'ai da 'yan kasuwar kasar da sauran su.
Wace matsala wannan yakin ya jawo ma duniya?
Wannan mataki ya kara sa farashin mai da suaran kayan abinci hauhawa a duniya. Kasashen Amurka da Burtaniya sun mika kokon baransu ga wasu kasashe masu arzikin man fetur kamar Saudiyya da Burtnaiya ta nemi ta kara yawan man da ta ke hakowa a kwanan nan, sai kuma dangantakar Amurka da Venezuela da ta dade da yin tsami amma kuma Amurka na ta zawarcin gwamnatin kasar domin samun matsaya daya akan sayar mata da mai.

Getty images
Yadda farashin abinci zai iya karuwa a duniya
Kasar Ukraine ce ta daya wajen samar da kashi 30 na alkamar duniya. Hakan ya sa farashin alkama ya kara tashi, wanda wannan na iya shafar kasashen dama.

Getty images
Yanzu haka akwai kasashen da wannan ta soma shafuwar tattalin arzikinsu. Kwanan nan kasashen Afirka irin Masar da Nijar da Mali da Tunisiya da wasu kasashen Asiya kamar Malesiya da Indunisiya suka kara farashin buredi da sauran kayan da akan sarrafa da alkama kamar biskit da fankaso da fankeke da sauran su. A makon jiya ma sai da aka yi wata zanga-zanga a Sudan sakamakon farashin buredi da ya yi tashin gwauron zabo mai alaka da karancin alkama a duniya.
Getty images
Haka ma kasar Aljeriya ta bayar da sanarwar dakatar da sayar da sukari da nau'in kayan abinci ga sauran kasashe makwabta a dalilin tsadar kayan sarrafa su da kuma karancin su da duniya ke fuskanta sakamakon wannan yaki.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

NDE Commences Sustainable Training and Loan Disbursement To 100 Youths in Sokoto

The National Directorate of Employment (NDE) has commenced Sustainable Agricultural Development Scheme (SADTS) and loand disbursement to 100 youths in Sokoto. Director-General of NDE, Malam Abubakar Fikpo, disclosed this on Tuesday in Sokoto during the orientation of agricultural loans disbursement held at Shamsuddeen Plaza. Fikpo represented by the Sokoto State NDE Coordinator Mrs Eunice J. Danmallam, said beneficiaries are entitled to N100,000 each at 9 per cent interest rate. He said the beneficiaries were captured under the Agricultural Enhancement Scheme (AES) and Community-Based Agricultural Empowerment Scheme (CBAES). He added they were also under Graduate Agricultural Empowerment Scheme (GAES) and Sustainable Agricultural Development and Empowerment Scheme (SADES). Fikpo said that six months moratorium was given after which  beneficiaries were expected to repay the loan in installments over a period of three years. Dan Mallam expressed gr...

The Nigerian Governors Forum Describe The Militant Attack On Benue State Governor As Shocking

The Nigerian Governors Forum (NGF) has described the militant attack on the Benue State governor as "shocking" and "scary".  Governor Samuel Ortom's delegation was attacked by gunmen on Saturday on the Makurdi-Gboko road, when he visited his farm.  In a statement issued by the group's chairman and Ekiti State Governor Kayode Fayemi on Sunday, the NGF congratulated Ortom for the escape from the attack which it said was "scary and offensive".  Inspector General of Police Mohammed Adamu also condemned the attack and ordered that security be beefed up on the governor and an investigation launched.  "The NGF has said in a loud voice that efforts to rehabilitate Benue State will not succeed," the statement said.  "One of the relatives of a former governor of the state was recently killed. This kind of act of violence must be stopped for whatever reason to kill the people of Benue."