Skip to main content

Shugaban Rasha Ya Nunawa Biden Yatsa

ewn.co.za
Shugaban kasar Rasha Vladimir Putin ya ce kalaman da shugaban Amurka Joe Biden ya yi ba za su tafi a banza ba. Yana dai mayar da martani ne akan kalaman shugaba Amurka da ya ce, "Putin azzalumi ne kuma wanda ya aikata manyan laifukan yaki".

Sai dai shugaba Putin ya ce ba za ta taba yuwa Rasha ta yafe ma Amurka ta kowane fanni ba sakamakon wadannan kalamai da ya kira, "na cin zarafin kasarsa".
Yanzu haka dai yakin da kasashen Ukraine da Rasha ke ci gaba da gwabzawa ya shiga mako na uku in da munana hare-haren da dakarun Rasha ke kaiwa suka yi sanadiyyar hallakar fararen hula da dama, ciki kuwa har da yara kanana.
npr.org
Kasashen da ke karkashin kungiyar tsaro ta NATO sun zakuda gefe guda ba tare da amincewa su tsunduma cikin yakin ba, in da suka bayar da hujjar cewa tsunduma yakin na iya haifar da yakin duniya na uku. Sai dai a maimakon haka sun tsananta sakawa Rasha karin takunkumai da suka hada da kin sayen man da ta ke hakowa, da rufe asusun ajiyar manyan jami'ai da 'yan kasuwar kasar da sauran su.
Wace matsala wannan yakin ya jawo ma duniya?
Wannan mataki ya kara sa farashin mai da suaran kayan abinci hauhawa a duniya. Kasashen Amurka da Burtaniya sun mika kokon baransu ga wasu kasashe masu arzikin man fetur kamar Saudiyya da Burtnaiya ta nemi ta kara yawan man da ta ke hakowa a kwanan nan, sai kuma dangantakar Amurka da Venezuela da ta dade da yin tsami amma kuma Amurka na ta zawarcin gwamnatin kasar domin samun matsaya daya akan sayar mata da mai.

Getty images
Yadda farashin abinci zai iya karuwa a duniya
Kasar Ukraine ce ta daya wajen samar da kashi 30 na alkamar duniya. Hakan ya sa farashin alkama ya kara tashi, wanda wannan na iya shafar kasashen dama.

Getty images
Yanzu haka akwai kasashen da wannan ta soma shafuwar tattalin arzikinsu. Kwanan nan kasashen Afirka irin Masar da Nijar da Mali da Tunisiya da wasu kasashen Asiya kamar Malesiya da Indunisiya suka kara farashin buredi da sauran kayan da akan sarrafa da alkama kamar biskit da fankaso da fankeke da sauran su. A makon jiya ma sai da aka yi wata zanga-zanga a Sudan sakamakon farashin buredi da ya yi tashin gwauron zabo mai alaka da karancin alkama a duniya.
Getty images
Haka ma kasar Aljeriya ta bayar da sanarwar dakatar da sayar da sukari da nau'in kayan abinci ga sauran kasashe makwabta a dalilin tsadar kayan sarrafa su da kuma karancin su da duniya ke fuskanta sakamakon wannan yaki.

Comments

Popular posts from this blog

Iran seeks talks with us after threat of attack – Trump

U.S. President Donald Trump has said that Iranian authorities have contacted the United States to seek talks, following his threat to take military action over the killing of protesters in the country. Trump made the statement while speaking to journalists, saying that a meeting between the two sides has already been planned, but that the United States might take some action before the meeting takes place. Meanwhile, a human rights organization in Iran says it has confirmed the deaths of nearly 500 people since the outbreak of the protests. Likewise, some circulating video clips show a site outside Iran where bodies are being kept, with people going there to search for the remains of their relatives who have gone missing.

WHEN LIES GO VIRAL: DEFENDING TRUTH IN NIGERIA AND WEST AFRICA’S DIGITAL PUBLIC SPHERES

Across Nigeria and West Africa, digital technology has reshaped how citizens engage with information, governance, and public debate. Mobile phones and social media platforms have become dominant sources of news, especially for young people and communities with limited access to traditional media. While this transformation has expanded civic participation and freedom of expression, it has also intensified the spread of misinformation, posing serious risks to democracy, public health, and social cohesion. Misinformation is no longer a marginal problem. It is a structural challenge that affects elections, security, development communication, and trust in public institutions. Addressing it requires coordinated action that combines ethical journalism, media literacy, platform accountability, and evidence based policy responses. THE DIGITAL INFORMATION LANDSCAPE IN NIGERIA AND WEST AFRICA Nigeria is Africa’s most populous country and one of its most digitally active societies. So...

Murtala Abdulkadir Dan Iya Gambun Sakkwatawa

Alhaji Murtala Abdulkadir Dan Iya ya shahara wajen ayyukan jinƙai a Jihar Sokoto tsawon  shekarun ya zuwa yanzu. Alhaji Murtala Abdulkadir Dan Iya shugaban Hukumar Bayar Da Tallafin Ƙaro Karatu ta Jihar Sokoto  A tattaunawar da jaridar Tantabara News ta yi da Nura Muhammad Chiso, wanda ke jagorancin daya daga cikin ƙungiyoyin Alhaji Murtala Abdulkadir Dan Iya, mai suna da ke bayar da tallafi da wayar da kan al'umma a jihar ta Sokoto, ya bayyana tarin manyan tallafan da wannan shahararren ɗan kasuwa, kuma ɗan siyasa ya yi wa dubban mutane mabukata a jihar, lamarin da ya ƙara ɗaukaka darajar sunansa a cikin jihar da ma wajenta. N ura Muhammad Chiso  Nura Muhammad Chiso ya ce, "wannan aikin alheri na shugaban Hukumar Bayar Da Tallafin Ƙaro Karatu ta Jihar Sokoto, wani babban aikin alheri ne da ya gane dubban jama'a talakawa har hakan ya sa suke kiran sa da gambun Sakkwatawa saboda faranta musu rai da yake yi". Ga wa...