Skip to main content

Buhari Ya Ce Maimala Ne Shugaban APC

A wani abu da ake ganin kamar zai iya haddasa sabuwar baraka a cikin jam'iyyar APC, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya shawarci gwamnonin APC su bar gwamnan jahar Yobe Maimala Buni ya dore kan shugabancin jam'iyyar.
Gwamnan dai ya isa birnin Landan tare da rakiyar Ministan ilmi Malam Adamu Adamu, in da kuma ya gana da shugaban kasar. A farkon makon jiya dai ne wasu jiga-jigan jam'iyyar APC suka maye gurbinsa da gwamnan jahar Naija Abubakar Sani Bello, wanda nan take ya rantsar shugabannin kwamitin gudanane da babban zaben jam'iyyar na kasa da ane sa ran yi a ranar 26 ga wannan wata na Maris.
An jiyo gwamnan jahar Kaduna Nasir El-Rufa'i a wata hira da tashar talabijin ta Channels na cewa, gwamnan jahar Naija ne ya samu sahakewar shugaban kasa.
El-Rufa'i ya ce, sun kafa wani kwamiti da suka tuntubi shugaban kasar, in da kuma ya amince da Sani Bello a matsayin halastaccen shugaban jam'iyyar APC na kasa.
A ganin masana, wasu na amfani da sunan shugaba Buhari wajen juya akalar gwamnati ko cimma wani buri na kashin kai, hanin yadda kowane bangare ke fitowa yana bayyana cewa Buhari ne ya goyi bayan bangarensa.
Wannan dai a cewar masu lura da al'amurran yau da kullum a Najeriya, ba zai haifar da kome ba face rabuwar kai, a daidai lokacin da babban zaben kasar ke karatowa.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Da Dumi Dumi An Ceto Yaran Da Aka Sace A Katsina

Sakataren gwamnatin jahar Katsina Alhaji Mustapha Inuwa ya fitar da sanarwar cewa an samu nasarar ceto daliban nan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su daga makarantar kwanan ta Kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina. Ya ce an ceto yaran su 340, kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta isowa jahar daga Tsafen jahar Zamfara. Ana sa ran gobe jumu'a za su gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kafin daga bisani a sada su da iyayensu. Sauran bayani zai zo nan gaba.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey