Skip to main content

An Hana Masu Mukaman Siyasa Jefa Kuri'a A Babban Taron APC Na Kasa

Kwamitin tsare-tsare na musamman na riko na jam’iyyar APC ya kori masu rike da mukaman siyasa daga kada kuri’a a babban taron kasa na ranar Asabar.

A cikin wata sanarwa da kwamitin ya fitar a ranar Alhamis, ya bayyana karara cewa “dukkan wadanda aka nada a siyasance da aka zaba a matsayin wakilai a babban taron kasa da aka shirya gudanarwa a ranar 26/3/2022, ba za su kada kuri’a ba bisa la’akari da cece-kucen da ke tattare da sashe na 84 (12) na dokar zabe.  2022."


Komitin, duk da haka, ya bayyana cewa masu nadin siyasa na iya halarta a matsayin masu sa ido kawai amma kada su dada kada su rage.

Hakan ya biyo bayan amincewar da Majalisar Dokoki ta kasa baki daya ta yi da dokar gyaran dokar zabe da shugaban kasa Muhammadu ya sanya wa hannu

Alamu sun bayyana a ranar Larabar da ta gabata ne shugaban kasa da gwamnonin jam’iyyar APC suka amince da batun fitowar jami’an jam’iyyar, ciki har da shugaban jam’iyyar na kasa.

A jiya alhamis shugaba Muhammadu Buhari ya gana da gwamnonin APC in da suka daddale matsaya tare da gindaya nasu sharudda da kuma shugaban kasar ya amince da su
Wannan ya nuna kusan jam'iyyar ta dunke barakar da ke son kunno kai cikin ta ana sauran kwana daya ta gudanar da babban taronta na kasa da zai haska makomar jam'iyyar nan gaba.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

An Sako Ƙarin Fasinjojin Jirgin Ƙasa Bakwai Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Wasu fasinjoji bakwai da aka yi garkuwa da su a harin jirgin kasa na ranar 28 ga Maris a jihar Kaduna sun samu 'yanci. An sako mutanen ne a safiyar Laraba bayan sun shafe kwanaki 135 a hannun ‘yan ta’addan. Sai dai ba a bayyana ko an biya kudin fansa ga 'yan ta'addar domin a sako su ba. Ɗaya daga waɗanda suka shiga sasantawar mai suna Tukur Mamu, ya fada  a wata sanarwa a ranar Laraba cewa shida daga cikin wadanda aka sako ‘yan gida daya ne, wadanda suka hada da ma’aurata da ‘ya’yansu hudu.  Sanarwar ta ce an sako yaran da iyayensu ne bayan da Sheik Ahmad Gumi ya shiga tsakani

Wanene Ɗan Jarida?

Ɗan jarida mutum ne kamar kowa, sai dai tunaninsa da manufofinsa kan tafi daidai ne kawai da ra'ayin MASU SAURARO ta fuskokin da suka shafi aikinsa. Ya zama mai wakiltar waɗanda ba su da baki ne ko kafafuwan zuwa, kuma idanuwan talakawa a kowane lokaci. Idan ka nuna ma sa launi shuɗi, ƙoƙarin ya ke ya tabbatar da launin nan shuɗi ne ziryan ko yana da garwaye? Idan ka ce ma sa labarin abu kaza ya faru, ba zai ce a'a ba kuma ba zai ce eh ba, aikinsa shi ne TABBATARWA . Idan mai sauraro namiji ne ko mace ko mai ra'ayin wani addini ko akida ko mai kuɗi ko talaka, ɗan jarida kan GIRMAMA kowa, kuma zai ɗauki kowa a matsayin DAIDAI ta fuskar ba su damar bayyana ra'ayoyinsu. Ɗan jarida kan tafi da zamani, ya kuma rungumi fasahar da ƘIRƘIRA ta kawo domin tafiya daidai lokaci. A kowace marra GASKIYA ita ce madogarar ɗan jarida, kuma wannan kan ƙara sa masu sauraro su amince da shi. Amma kuma, dole ne ɗan jarida ya zama MAI IKON KANSA , ba zai yi ma kowa alfarma b...