Skip to main content

Abduljabbari Ya Ce Idan An Ba Shi Sarari Zai Tuba

 Abduljabbari ya koka a kan yadda mukabalar ke tafiya, duk da ya kasa amsa muhimman tambayoyin da aka yi masa.
Ya ce mintina 10 da aka ba shi don ya amsa tambayoyin da suka shafi cin zarafin Annabi (s.a.w.) ba za su isa ya kwance littafai kusan 500 da ya zo da su ba.
An tambai shi ko a wane hadisi aka kira annabi bunsuru ko arne?
Ya ce idan an ba shi karin lokaci zai binciko hadisan ya zo da su amma yanzu an kure shi ba cikin shiri yake ba, kuma gaba daya a cewar sa, babu gaskiya a mukabalar. Ya ce yana son ne ya tsamo mutane daga halakar da ke sa suna yin ridda sakamako rudanin hadisan.
Kasancewar wannan kasawa ya sa daya daga Malaman da ke zurara masa tambayoyi Malam Abubakar Madatai ya neme shi da ya tuba ya tabbatar da kuskuren da ya yi.
Amma Abduljabbar ya ce ta ya zai tuba a wajen wannan muƙabala, a gaban kowa da kowa, ba tare da ba shi karin lokaci don haduwa ta gaba ba, sannan a ba shi karin wasu hujjoji da suka fi nasa.
 Da ya ki tuba, malamin na bangaren Tijjaniya ya kuma nemi ya yi bayani a wane hadisi aka ambaci cewa annabi (s.a.w.) ya sha giya a lokacin aurensa Nana Khadija, da kuma tambayar da Malam Mahmud Hotoro Kano ya sake yi masa na karin haske akan kiran annabi da bamaguje da aka yi,  dukan su dai ya ce ba a fahimce shi ba kuma ya na so a sake saka wata sabuwar rana don ya shirya.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Da Dumi Dumi An Ceto Yaran Da Aka Sace A Katsina

Sakataren gwamnatin jahar Katsina Alhaji Mustapha Inuwa ya fitar da sanarwar cewa an samu nasarar ceto daliban nan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su daga makarantar kwanan ta Kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina. Ya ce an ceto yaran su 340, kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta isowa jahar daga Tsafen jahar Zamfara. Ana sa ran gobe jumu'a za su gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kafin daga bisani a sada su da iyayensu. Sauran bayani zai zo nan gaba.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey