Skip to main content

Abduljabbari Ya Kasa Kare Kansa

Shugaban Sashen Nazarin Addinin Musulunci na Jami'ar Bayaro da ke Kano, Farfesa Salisu Shehu, yace baya ga kame-kame da Abduljabbar ke yi babu wata tambaya daya tak da ya amsa.
Ya kara da cewa a maimakon ya bude wagagen littafan nan da ya zo da su don fiddo da hujja sai kawai ya ce babu lokaci. A kan hala ya yanke hukuncin cewa Abduljabbar Nasiru Kabara ya kasa kare kansa.
A na sa bangare Abduljabbar ya nemi a dai sake ba shi wani lokaci, watakila idan ya shirya, kuma ga hujja, zai iya tuba.
Sai dai Malam Abubakar Madatai, daya daga masu gudanar da muhawarar, ya roki a sake ba Abduljabbar karin lokacin ya ke ta bukata. Su sun shirya amma ya ce shi bai shirya ba don haka a ba shi karin lokacin, kazalika ya nemi gwamnatin jahar Kano da nan gaba idan an amince da bukatar to a bada damar watsawa a gidajen rediyo da talabijin kowa ya ji ya gani.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey