Skip to main content

Kasar Isra'ila Na Kaiwa 'Yan Jarida Hari

 GAZA: Wani hari ta sama da Isra’ila ta kai ya lalata wani dogon gini a birnin Gaza wanda ke dauke da ofisoshin kamfanin dillacin labarai na Associated Press da sauran kafafen yada labarai a yau Asabar, wannan farmakin sojin ya zo ne kwatsam ba tare da yin gargadi ga mazauna ginin ba, matakin da sojoji suka dauka na yin shiru a yayin fafatawarsu da kungiyar Hamas.
Harin ta sama ya zo ne kasa da sa'a guda bayan da sojojin suka umarci mutane su fice daga ginin, wanda kuma ya hada da Al-Jazeera, da sauran ofisoshi da gidajen jama'a. Karfin harin ya ruguje daukacin ginin mai hawa 12, qanda ya haddasa turnukewar ƙura.  Babu wani bayani akan dalilin da ya sa aka kai harin.
 
Wannan sabon farmakin na zuwa ne sa’o’i bayan da wani harin sama da Isra’ila ta kai a wani sansanin ‘yan gudun hijira da ke da yawan jama’a a garin na Gaza da ya kashe Falasdinawa akalla 10 'yan asalin dangi daya, wadanda galibinsu kananan yara ne, a wani hari mafi muni da aka kai a rikicin da ke wakana yanzu.  
Duka bangarorin biyu sun matsa lamba don cin nasara yayin da kokarin tsagaita wuta ya gagara. 
Barkewar rikici na baya-bayan nan ya fara ne daga Kudus kuma ya bazu a yankin, inda arangamar yahudawa da Larabawa da tarzoma a garuruwa masu hade da Isra’ila ke ci gaba da yaduwa. 
Haka nan kuma an yi zanga-zangar Falasdinawa da yawa a ranar Juma’a da yau din nan a Yammacin Gabar Kogin Jodan, yankin da sojojin Isra’ila suka harbe kimanin Falasdinawa 11.

Comments

Popular posts from this blog

Iran seeks talks with us after threat of attack – Trump

U.S. President Donald Trump has said that Iranian authorities have contacted the United States to seek talks, following his threat to take military action over the killing of protesters in the country. Trump made the statement while speaking to journalists, saying that a meeting between the two sides has already been planned, but that the United States might take some action before the meeting takes place. Meanwhile, a human rights organization in Iran says it has confirmed the deaths of nearly 500 people since the outbreak of the protests. Likewise, some circulating video clips show a site outside Iran where bodies are being kept, with people going there to search for the remains of their relatives who have gone missing.

WHEN LIES GO VIRAL: DEFENDING TRUTH IN NIGERIA AND WEST AFRICA’S DIGITAL PUBLIC SPHERES

Across Nigeria and West Africa, digital technology has reshaped how citizens engage with information, governance, and public debate. Mobile phones and social media platforms have become dominant sources of news, especially for young people and communities with limited access to traditional media. While this transformation has expanded civic participation and freedom of expression, it has also intensified the spread of misinformation, posing serious risks to democracy, public health, and social cohesion. Misinformation is no longer a marginal problem. It is a structural challenge that affects elections, security, development communication, and trust in public institutions. Addressing it requires coordinated action that combines ethical journalism, media literacy, platform accountability, and evidence based policy responses. THE DIGITAL INFORMATION LANDSCAPE IN NIGERIA AND WEST AFRICA Nigeria is Africa’s most populous country and one of its most digitally active societies. So...

Murtala Abdulkadir Dan Iya Gambun Sakkwatawa

Alhaji Murtala Abdulkadir Dan Iya ya shahara wajen ayyukan jinƙai a Jihar Sokoto tsawon  shekarun ya zuwa yanzu. Alhaji Murtala Abdulkadir Dan Iya shugaban Hukumar Bayar Da Tallafin Ƙaro Karatu ta Jihar Sokoto  A tattaunawar da jaridar Tantabara News ta yi da Nura Muhammad Chiso, wanda ke jagorancin daya daga cikin ƙungiyoyin Alhaji Murtala Abdulkadir Dan Iya, mai suna da ke bayar da tallafi da wayar da kan al'umma a jihar ta Sokoto, ya bayyana tarin manyan tallafan da wannan shahararren ɗan kasuwa, kuma ɗan siyasa ya yi wa dubban mutane mabukata a jihar, lamarin da ya ƙara ɗaukaka darajar sunansa a cikin jihar da ma wajenta. N ura Muhammad Chiso  Nura Muhammad Chiso ya ce, "wannan aikin alheri na shugaban Hukumar Bayar Da Tallafin Ƙaro Karatu ta Jihar Sokoto, wani babban aikin alheri ne da ya gane dubban jama'a talakawa har hakan ya sa suke kiran sa da gambun Sakkwatawa saboda faranta musu rai da yake yi". Ga wa...