Skip to main content

Malami Ya Ce Zai Bi Umurnin Kotu Ya Goge Sashe na 84 (12)

Ministan shari'ar Najeriya Abubakar Malami ya ce cikin gaggawa zai bi umurnin wata babbar kotun Najeriya da ta bukaci a goge sashe na 84 da ya tilasta duk masu rike mukaman siyasa aje mukamansu kwana 30 kafin zabe.
KUNA IYA KARANTA:
Malami dai ya tabbatar da cewa, zai yi ma dokar gyaran fuska. Tun da farko dai shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sanyawa dokar hannu tare da rokon 'yan majalisar dattawan Najeriya da su yi ma ta kwaskwarima wajen cire wannan sashe, amma suka ki amincewa da wannan bukata.
Wannan na zuwa ne kwanaki kalilan kafin gudanar da babban zaben jam'iyyar APC da zai gudana a ranar 26 ga wannan wata na Maris. Kuma a na ganin zai iya kara haifar da baraka cikin jam'iyyar.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Da Dumi Dumi An Ceto Yaran Da Aka Sace A Katsina

Sakataren gwamnatin jahar Katsina Alhaji Mustapha Inuwa ya fitar da sanarwar cewa an samu nasarar ceto daliban nan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su daga makarantar kwanan ta Kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina. Ya ce an ceto yaran su 340, kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta isowa jahar daga Tsafen jahar Zamfara. Ana sa ran gobe jumu'a za su gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kafin daga bisani a sada su da iyayensu. Sauran bayani zai zo nan gaba.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey