Skip to main content

Illolin Amfani Da Rikitacciyar Jimla A Rubutu Ko Rediyo

Papertrue.blog
*"A kokarin hada su da 'yan'uwansu da sanadiyyar rikice-rikice suka rabu."

A yadda harshe ya ke da wuyar sha'ani wajen aikewa da sako, wajibi ne a kaucewa kowace irin jimla mai harshen damo ko mai iya haddasa rudani a kwalkwalwar mai karatu ko saurare.
A maimakon haka ya fi dacewa a ce, "A kokarin hada su da 'yan'uwansu da tashe-tashen hankula suka raba"

Dalili kuwa kalamar rikici ba ta dace da nan ba saboda ko mutum biyu na iya rikici da juna. 
Rikici na nufin jayayya ko rashin yarda da abu da zai iya haifar da rashin matsaya daya, wanda kuma zai kai ga fada. Mutane na iya yin gaba da juna akan rikici na siyasa ko gado.

Amma ita kalmar tashin hankali a bayyane ta ke ga mai saurare, sakamakon irin yadda kalmar ta zama tamkar ta yi kaka-gida saboda yadda yankunan arewacin Najeriya ke fama da tashe-tashen hankula.

Me Ya Kawo Rudani A Nan?
A jimla ta farko mai saurare zai dauka rikicin tsakanin 'yan'uwan ya ke, amma a jimla ta biyu an lura cewa tashin hankalin da ya faru ne ya raba su.
Wace Illa Hakan Kan Jawo?
Sau tari mai karatu ko saurare na iya kasa fahimtar in da maganar ta dosa, saboda ba a fayyace ma'anarta a fili ba.
Misali idan ka ce, "Bala Ya karya ma ta masara".
Za ka saka mai saurare ko karatu a rudu kasancewar ba ka fayyace wanda ya mallaki masarar ba.
Zai fi dacewa ka ce, "Bala ya karya masarar Kande, Ko Bala ya karya ma Kande masararsa".
Fakat!

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Da Dumi Dumi An Ceto Yaran Da Aka Sace A Katsina

Sakataren gwamnatin jahar Katsina Alhaji Mustapha Inuwa ya fitar da sanarwar cewa an samu nasarar ceto daliban nan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su daga makarantar kwanan ta Kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina. Ya ce an ceto yaran su 340, kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta isowa jahar daga Tsafen jahar Zamfara. Ana sa ran gobe jumu'a za su gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kafin daga bisani a sada su da iyayensu. Sauran bayani zai zo nan gaba.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey