Skip to main content

Illolin Amfani Da Rikitacciyar Jimla A Rubutu Ko Rediyo

Papertrue.blog
*"A kokarin hada su da 'yan'uwansu da sanadiyyar rikice-rikice suka rabu."

A yadda harshe ya ke da wuyar sha'ani wajen aikewa da sako, wajibi ne a kaucewa kowace irin jimla mai harshen damo ko mai iya haddasa rudani a kwalkwalwar mai karatu ko saurare.
A maimakon haka ya fi dacewa a ce, "A kokarin hada su da 'yan'uwansu da tashe-tashen hankula suka raba"

Dalili kuwa kalamar rikici ba ta dace da nan ba saboda ko mutum biyu na iya rikici da juna. 
Rikici na nufin jayayya ko rashin yarda da abu da zai iya haifar da rashin matsaya daya, wanda kuma zai kai ga fada. Mutane na iya yin gaba da juna akan rikici na siyasa ko gado.

Amma ita kalmar tashin hankali a bayyane ta ke ga mai saurare, sakamakon irin yadda kalmar ta zama tamkar ta yi kaka-gida saboda yadda yankunan arewacin Najeriya ke fama da tashe-tashen hankula.

Me Ya Kawo Rudani A Nan?
A jimla ta farko mai saurare zai dauka rikicin tsakanin 'yan'uwan ya ke, amma a jimla ta biyu an lura cewa tashin hankalin da ya faru ne ya raba su.
Wace Illa Hakan Kan Jawo?
Sau tari mai karatu ko saurare na iya kasa fahimtar in da maganar ta dosa, saboda ba a fayyace ma'anarta a fili ba.
Misali idan ka ce, "Bala Ya karya ma ta masara".
Za ka saka mai saurare ko karatu a rudu kasancewar ba ka fayyace wanda ya mallaki masarar ba.
Zai fi dacewa ka ce, "Bala ya karya masarar Kande, Ko Bala ya karya ma Kande masararsa".
Fakat!

Comments

Popular posts from this blog

Iran seeks talks with us after threat of attack – Trump

U.S. President Donald Trump has said that Iranian authorities have contacted the United States to seek talks, following his threat to take military action over the killing of protesters in the country. Trump made the statement while speaking to journalists, saying that a meeting between the two sides has already been planned, but that the United States might take some action before the meeting takes place. Meanwhile, a human rights organization in Iran says it has confirmed the deaths of nearly 500 people since the outbreak of the protests. Likewise, some circulating video clips show a site outside Iran where bodies are being kept, with people going there to search for the remains of their relatives who have gone missing.

WHEN LIES GO VIRAL: DEFENDING TRUTH IN NIGERIA AND WEST AFRICA’S DIGITAL PUBLIC SPHERES

Across Nigeria and West Africa, digital technology has reshaped how citizens engage with information, governance, and public debate. Mobile phones and social media platforms have become dominant sources of news, especially for young people and communities with limited access to traditional media. While this transformation has expanded civic participation and freedom of expression, it has also intensified the spread of misinformation, posing serious risks to democracy, public health, and social cohesion. Misinformation is no longer a marginal problem. It is a structural challenge that affects elections, security, development communication, and trust in public institutions. Addressing it requires coordinated action that combines ethical journalism, media literacy, platform accountability, and evidence based policy responses. THE DIGITAL INFORMATION LANDSCAPE IN NIGERIA AND WEST AFRICA Nigeria is Africa’s most populous country and one of its most digitally active societies. So...

Murtala Abdulkadir Dan Iya Gambun Sakkwatawa

Alhaji Murtala Abdulkadir Dan Iya ya shahara wajen ayyukan jinƙai a Jihar Sokoto tsawon  shekarun ya zuwa yanzu. Alhaji Murtala Abdulkadir Dan Iya shugaban Hukumar Bayar Da Tallafin Ƙaro Karatu ta Jihar Sokoto  A tattaunawar da jaridar Tantabara News ta yi da Nura Muhammad Chiso, wanda ke jagorancin daya daga cikin ƙungiyoyin Alhaji Murtala Abdulkadir Dan Iya, mai suna da ke bayar da tallafi da wayar da kan al'umma a jihar ta Sokoto, ya bayyana tarin manyan tallafan da wannan shahararren ɗan kasuwa, kuma ɗan siyasa ya yi wa dubban mutane mabukata a jihar, lamarin da ya ƙara ɗaukaka darajar sunansa a cikin jihar da ma wajenta. N ura Muhammad Chiso  Nura Muhammad Chiso ya ce, "wannan aikin alheri na shugaban Hukumar Bayar Da Tallafin Ƙaro Karatu ta Jihar Sokoto, wani babban aikin alheri ne da ya gane dubban jama'a talakawa har hakan ya sa suke kiran sa da gambun Sakkwatawa saboda faranta musu rai da yake yi". Ga wa...