Skip to main content

Illolin Amfani Da Rikitacciyar Jimla A Rubutu Ko Rediyo

Papertrue.blog
*"A kokarin hada su da 'yan'uwansu da sanadiyyar rikice-rikice suka rabu."

A yadda harshe ya ke da wuyar sha'ani wajen aikewa da sako, wajibi ne a kaucewa kowace irin jimla mai harshen damo ko mai iya haddasa rudani a kwalkwalwar mai karatu ko saurare.
A maimakon haka ya fi dacewa a ce, "A kokarin hada su da 'yan'uwansu da tashe-tashen hankula suka raba"

Dalili kuwa kalamar rikici ba ta dace da nan ba saboda ko mutum biyu na iya rikici da juna. 
Rikici na nufin jayayya ko rashin yarda da abu da zai iya haifar da rashin matsaya daya, wanda kuma zai kai ga fada. Mutane na iya yin gaba da juna akan rikici na siyasa ko gado.

Amma ita kalmar tashin hankali a bayyane ta ke ga mai saurare, sakamakon irin yadda kalmar ta zama tamkar ta yi kaka-gida saboda yadda yankunan arewacin Najeriya ke fama da tashe-tashen hankula.

Me Ya Kawo Rudani A Nan?
A jimla ta farko mai saurare zai dauka rikicin tsakanin 'yan'uwan ya ke, amma a jimla ta biyu an lura cewa tashin hankalin da ya faru ne ya raba su.
Wace Illa Hakan Kan Jawo?
Sau tari mai karatu ko saurare na iya kasa fahimtar in da maganar ta dosa, saboda ba a fayyace ma'anarta a fili ba.
Misali idan ka ce, "Bala Ya karya ma ta masara".
Za ka saka mai saurare ko karatu a rudu kasancewar ba ka fayyace wanda ya mallaki masarar ba.
Zai fi dacewa ka ce, "Bala ya karya masarar Kande, Ko Bala ya karya ma Kande masararsa".
Fakat!

Comments

Wadanda aka fi karantawa

WHEN LIES GO VIRAL: DEFENDING TRUTH IN NIGERIA AND WEST AFRICA’S DIGITAL PUBLIC SPHERES

Across Nigeria and West Africa, digital technology has reshaped how citizens engage with information, governance, and public debate. Mobile phones and social media platforms have become dominant sources of news, especially for young people and communities with limited access to traditional media. While this transformation has expanded civic participation and freedom of expression, it has also intensified the spread of misinformation, posing serious risks to democracy, public health, and social cohesion. Misinformation is no longer a marginal problem. It is a structural challenge that affects elections, security, development communication, and trust in public institutions. Addressing it requires coordinated action that combines ethical journalism, media literacy, platform accountability, and evidence based policy responses. THE DIGITAL INFORMATION LANDSCAPE IN NIGERIA AND WEST AFRICA Nigeria is Africa’s most populous country and one of its most digitally active societies. So...