Skip to main content

El-Rufai Ya Mika Kokon Bara Ga JAMB Kan Kada Ta Sassautawa Dalibai

Daga Zubairu Ahmad Bashir
Gwamnan Jahar Kaduna Malam Nasiru El-Rufa'i ya mika kokon baransa ga Hukuma Shirya Jarrabawar Share Fagen Shiga Jami'a (JAMB) da ta duna rokonsa kada ta ragewa daliban da ke son shiga jami'a makin da ake bukata kafin samun gurbi.

Gwamnan ya shaidawa gidan talabijin na Channels haka ne a wata hira da aka yi da shi. Ya ce ko kusa ba taimakawa daliban hakan zai yi ba face mayar da su cima-kwance. El-Rufa'i ya kara da cewa yankin arewacin Najeriya na cikin halin koma baya a bangaren ilmi kuma tuni aka yi masa zarra a wannan fanni.

A cikin hirar ya roki hukumar ta JAMB Allah-Ma'aiki da kada ta sassautawa kowane dalibi. Abu mafi kyau in ji shi shine su ci jarrabawar da za ta ba su makin da za su iya samun gurbin karatu a jami'o'i da manyan kwalejojin Najeriya.
Idan ana iya tunawa dai an samu mummunar faduwar jarrabawar share fagen shiga jami'a ta bana, in da galibin wadanda suka zana ta suka kasa samun adadin makin da zai ba iya ba su gurbi. 
Wanda wannan ya sa hukumar ta JAMB ta ba jami'o'i damar kayyade makin da za su ba dalibai gurabun karo karatu  da kan su ba  tare da ita hukumar ta kayyade munsu ba.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

An Sako Ƙarin Fasinjojin Jirgin Ƙasa Bakwai Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Wasu fasinjoji bakwai da aka yi garkuwa da su a harin jirgin kasa na ranar 28 ga Maris a jihar Kaduna sun samu 'yanci. An sako mutanen ne a safiyar Laraba bayan sun shafe kwanaki 135 a hannun ‘yan ta’addan. Sai dai ba a bayyana ko an biya kudin fansa ga 'yan ta'addar domin a sako su ba. Ɗaya daga waɗanda suka shiga sasantawar mai suna Tukur Mamu, ya fada  a wata sanarwa a ranar Laraba cewa shida daga cikin wadanda aka sako ‘yan gida daya ne, wadanda suka hada da ma’aurata da ‘ya’yansu hudu.  Sanarwar ta ce an sako yaran da iyayensu ne bayan da Sheik Ahmad Gumi ya shiga tsakani

Osinbajo Ya Fito Takarar Shugaban Kasa

A jiya ne mataimakin shugaban Najeriya, Farfesa Yemi Osinbajo ya bayyana aniyarsa ta tsaya takarar shugaban kasar Najeriya a 2023. Ya fadi hakan ne a lokacin wani kwarya-kwaryar buda baki da ya halarta tare da wasu gwamnonin jam'iyyar APC da suka hada da na jahar Kebi Abubakar Atiku Bagudo da na Kaduna Malam Nasiru El-Rufa'i da sauran su. A yau litinin dai ne Osinbajo zai sanar da wannan kudiri nasa a dokance, ta wani jawabi da za a yada ta bidiyo. Idan ana iya tunawa dai watanni biyu da suka gabata mataimakin shugaban Najeriyar ya ce ya sanar da shugaban kasa Muhammadu Buhari wannan manufa tasa. Kafin bayyana wannan bukata, tuni dai wasu suka fito suka bayyana bukatar tsayawa takarar kujerar shugaban kasa karkashin jam'iyyar APC da suka hada da tsohon gwamnan jahar Legas, Bola Ahmed Tinubu da gwamnan jahar Kogi Yahaya Bello da Rochas Okorocha da kuma kwanan nan ministan suhuri kuma tsohon gwamnan jahar Ribas, Rotimi Amechi da sauran su.