Skip to main content

El-Rufai Ya Mika Kokon Bara Ga JAMB Kan Kada Ta Sassautawa Dalibai

Daga Zubairu Ahmad Bashir
Gwamnan Jahar Kaduna Malam Nasiru El-Rufa'i ya mika kokon baransa ga Hukuma Shirya Jarrabawar Share Fagen Shiga Jami'a (JAMB) da ta duna rokonsa kada ta ragewa daliban da ke son shiga jami'a makin da ake bukata kafin samun gurbi.

Gwamnan ya shaidawa gidan talabijin na Channels haka ne a wata hira da aka yi da shi. Ya ce ko kusa ba taimakawa daliban hakan zai yi ba face mayar da su cima-kwance. El-Rufa'i ya kara da cewa yankin arewacin Najeriya na cikin halin koma baya a bangaren ilmi kuma tuni aka yi masa zarra a wannan fanni.

A cikin hirar ya roki hukumar ta JAMB Allah-Ma'aiki da kada ta sassautawa kowane dalibi. Abu mafi kyau in ji shi shine su ci jarrabawar da za ta ba su makin da za su iya samun gurbin karatu a jami'o'i da manyan kwalejojin Najeriya.
Idan ana iya tunawa dai an samu mummunar faduwar jarrabawar share fagen shiga jami'a ta bana, in da galibin wadanda suka zana ta suka kasa samun adadin makin da zai ba iya ba su gurbi. 
Wanda wannan ya sa hukumar ta JAMB ta ba jami'o'i damar kayyade makin da za su ba dalibai gurabun karo karatu  da kan su ba  tare da ita hukumar ta kayyade munsu ba.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey