Skip to main content

El-Rufai Ya Mika Kokon Bara Ga JAMB Kan Kada Ta Sassautawa Dalibai

Daga Zubairu Ahmad Bashir
Gwamnan Jahar Kaduna Malam Nasiru El-Rufa'i ya mika kokon baransa ga Hukuma Shirya Jarrabawar Share Fagen Shiga Jami'a (JAMB) da ta duna rokonsa kada ta ragewa daliban da ke son shiga jami'a makin da ake bukata kafin samun gurbi.

Gwamnan ya shaidawa gidan talabijin na Channels haka ne a wata hira da aka yi da shi. Ya ce ko kusa ba taimakawa daliban hakan zai yi ba face mayar da su cima-kwance. El-Rufa'i ya kara da cewa yankin arewacin Najeriya na cikin halin koma baya a bangaren ilmi kuma tuni aka yi masa zarra a wannan fanni.

A cikin hirar ya roki hukumar ta JAMB Allah-Ma'aiki da kada ta sassautawa kowane dalibi. Abu mafi kyau in ji shi shine su ci jarrabawar da za ta ba su makin da za su iya samun gurbin karatu a jami'o'i da manyan kwalejojin Najeriya.
Idan ana iya tunawa dai an samu mummunar faduwar jarrabawar share fagen shiga jami'a ta bana, in da galibin wadanda suka zana ta suka kasa samun adadin makin da zai ba iya ba su gurbi. 
Wanda wannan ya sa hukumar ta JAMB ta ba jami'o'i damar kayyade makin da za su ba dalibai gurabun karo karatu  da kan su ba  tare da ita hukumar ta kayyade munsu ba.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

NDE Commences Sustainable Training and Loan Disbursement To 100 Youths in Sokoto

The National Directorate of Employment (NDE) has commenced Sustainable Agricultural Development Scheme (SADTS) and loand disbursement to 100 youths in Sokoto. Director-General of NDE, Malam Abubakar Fikpo, disclosed this on Tuesday in Sokoto during the orientation of agricultural loans disbursement held at Shamsuddeen Plaza. Fikpo represented by the Sokoto State NDE Coordinator Mrs Eunice J. Danmallam, said beneficiaries are entitled to N100,000 each at 9 per cent interest rate. He said the beneficiaries were captured under the Agricultural Enhancement Scheme (AES) and Community-Based Agricultural Empowerment Scheme (CBAES). He added they were also under Graduate Agricultural Empowerment Scheme (GAES) and Sustainable Agricultural Development and Empowerment Scheme (SADES). Fikpo said that six months moratorium was given after which  beneficiaries were expected to repay the loan in installments over a period of three years. Dan Mallam expressed gr...

The Nigerian Governors Forum Describe The Militant Attack On Benue State Governor As Shocking

The Nigerian Governors Forum (NGF) has described the militant attack on the Benue State governor as "shocking" and "scary".  Governor Samuel Ortom's delegation was attacked by gunmen on Saturday on the Makurdi-Gboko road, when he visited his farm.  In a statement issued by the group's chairman and Ekiti State Governor Kayode Fayemi on Sunday, the NGF congratulated Ortom for the escape from the attack which it said was "scary and offensive".  Inspector General of Police Mohammed Adamu also condemned the attack and ordered that security be beefed up on the governor and an investigation launched.  "The NGF has said in a loud voice that efforts to rehabilitate Benue State will not succeed," the statement said.  "One of the relatives of a former governor of the state was recently killed. This kind of act of violence must be stopped for whatever reason to kill the people of Benue."