Skip to main content

Patience Jonathan Na Cikin Tsaka Mai Wuya

 

Mai shari’a T.G Ringim na babbar kotun tarayya da ke Legas ya tsayar da ranar 7 ga watan Oktoba, 2021, don sauraren karar da ke neman a kwace dala mikiyan 5.78 da wasu karin dala biiyan N2.4 da ke da nasaba da uwargidan tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan.

A ranar 26 ga watan  Afrilun shekarar 2017, mai shari'a Mojisola Olatoregun ta bayar da umarnin a kwace kudaden na wani dan lokaci bayan da Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta ce suna da alaka da zambar karkatar da kudade.

Hasalima, baya ga wani asusun Patience na sirri mai kimanin dala miliyan 5.78, alkalin ya kuma daskarar da wasu asusun da ke da nasaba da ita ciki har da wani asusun da ta ke a bankin Ecobank tare da ragowar wasu naira biliyan 2.4 da aka bude da sunan kamfunnan La Wari Furniture da Bath Limited.

Amma kokarin tabbatar da umurnin ya gamu da cikas kasancewar lauyan Patience, Ifedayo Adedipe (SAN) da Cif Mike Ozekhome (SAN), lauya ma kare kamfunnan La Wari Furniture da Bath Limited, sun nuna turjiya kan amincewa da shi.

Daga baya lauyoyin biyu sun daukaka kara, in da suke neman ta yi watsi da umarnin kwace kayayyakin na wani dan lokaci tare da kwato kudaden amma Kotun Kolin ta goyi bayan umarnin karamar kotun.

Duk da haka, a tsakiyar lokacin da aka kammala sauraren karar kan kudaden da aka ambata, mai shari'a Olatoregun ya yi ritaya daga daga muminsa a shekarar 2019.

Wannan lamarin ya tilasta wa Alkalin Kotun da ya sake tura batun zuwa ga Mai shari’a Chuka Obiozor don ya saurari hukuncin amma bai saurari karar ba kafin a tura shi Benin.

 A ci gaba da shari’ar a ranar Litinin, Lauyan EFCC, Rotimi Oyedepo, ya yi wa Mai Shari’a Ringim bayanin yadda lamarin ya ke, yayin da lauya mai kare Patience ya sanar da alkalin cewa an dage shari’ar don neman karin bayani saboda ta zo ne a karon farko a gabansa.

Lauyan kamfanonin a nasa bangaren ya bukaci kotun da ta dage shari’ar inda ya ke cewa ta dawo sabuwa fil kuma yana da niyyar shigar da takardar neman kalubalantar gaba dayan yadd aka gudanar da shari’ar.

Ya kuma bukaci kotun da ta ba da dogon lokaci don ba shi damar gabatar da takardar neman hakan.

Da yake amsawa, Oyedepo ya ki amincewa da bukatar sannan ya roki kotun da kar ta bayar da irin wannan a bisa hujjar cewa akwai wani tsari da aka shimfida a Sashe na 17 na Dokar Hukumar Yaki da Almubazzaranci da Dukiyar Jama'a da Sauran Laifuka, wadanda EFCC ta bi diddigi ya zuwa matakin da y sahalewa kotu damar kwace kudaden.

A kokacin zaman kotun Mai Shari'a Ringim ya bayyana cewa shari'ar na da matukar muhimmanci, babu wani mataki da zai iya kakubalantar ta 

 Ya ce, “A ra’ayina na tawali’u, akwai hanyar da za a bi  wajen daukan matakin kalubalantar hukunci ba lallai sai an dage shari'ar ba, wanda a wannan matsayi da aka kai kotu ba ta da qani hurumi na dage shari'ara

 “Amma, kuma kotun ba za ta hana bukatar ba, sakamakon haka, an umarci wanda ake kara na biyu da ya gabatar da bukatar, idan akwai, a cikin kwanaki 14 daga yau, kuma mai shigar da karar zai sami mako guda ya amsa.  Za a saurare shi tare da aiwatar da kudirin kwace kudaden, wanda kuma zai iya zama mataji na karshe.”in ji mai shari'a Ringim.

Mai shari'a Ringim ya dage zaman shari’ar har zuwa ranar 7 ga watan Oktoba, 2021.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

National Directorate of Employment (NDE) Disburses 100,000 as a Loan to 108 Agricultural Empowerment Scheme Beneficiaries in Sokoto

The state Coordinator of the agency said this was to enable the beneficiaries to be self reliant and contribute their quota to the development of the country. She said the programme was a combined orientation made up of 108 beneficiaries of Agricultural Empowerment Scheme, Community Based Agricultural Empowerment Scheme, Sustainable Agricultural Development Empowerment Scheme and Graduate Agricultural Empowerment Scheme that were given loans of N100, 000 each. Mrs. Danmallam added that the beneficiaries are graduates of NDE agricultural Extension, Poultry and Vegetable production. She said the money disbursed to them was a loan facility which would attract a single digit simple interest rate of 9 % and will have a moratorium of six months before beneficiaries will start paying back and it is repayable in three years.  Therefore, urged the them to ensure timely repayment to enable other unemployed persons to also benefit. In his goodwill message, ...

Wata Mota Cike Da Harsasan Bindiga Ta Fada Rami A Garin Awka Na Jahar Imo

Hankalin jama'a yayi matukar tashi a jiya Lahadi biyo bayan gano wata babbar mota cike da harsasai masu rai a birnin Anacha na jahar Imo da ke kudu maso gabashin tarayyar Najeriya. Rahotannin da suka shigo muna na cewa jami'an tsaron cikin hanzari sun afkawa garin na kasuwanci domin daukar matakin gaggawa kan lamarin.  Babbar motar wadda ke dauke da kwaliyoyin harsasai masu rai ta fada cikin wani rami da ke kan titi, inda dukan harsasan suka zube. Wata majiya da ta tabbatar da faruwar lamarin ta ce: “Motar ta fadi, kuma duk titin na cike da harsasai.  Wasu yaran ma sun debi wasu da hannayensu suka gudu, kafin jami’an tsaro su iso wurin. ”  Majiyar ta ci gaba da bayyana cewa direban babbar motar da mai yi masa hidima sun yi watsi da motar bayan hatsarin ya faru, inda suka yi batan dabo zuwa inda ba a sani ba. Amma wata majiyar ta ce ‘yan sanda sun cafke direban. “Lamarin ya jawo jami'an tsaro masu yawa zuwa yankin hanyar Awka da da safiyar yau. 'Yan sanda sun...

Biden Ya Doke Trump A Georgia Da Ratar Kuri'u 12,284

 An kammala kirga kuri'un jahar Georgia da ake takaddama kan ta, in da Joe Biden ya lashe jahar da rata mai yawa. Jahar Atlanta Georgia mai yawan kuri'u miliyan biyar da doriya ta zama sha kallo a idon duniya ganin yadda shugaba Donald Trump ya yi zargin shi ne ya samu nasara a jahar kuma ya nemi sai an sake kirga dukan kurin'un da aka kada. A jiya alhamis da yamma ne aka kammala lissafin da ya kwashe kusan fiye da mako daya a na yi, in da ofishin sakataren gwamnatin jahar ya fitar da wannan sanarwa. Ofishin Brad Raffensperger ya bayyana cewa bayan sake kirga dukan kuri'un da hannu, sakamakon da aka samu tun farko yana nan bai sauya ba. Joe Biden ya doke Donald Trump da yawan kuri'u 12,284, yayin da shugaba Donald Trump ya samu 1,872.

An Ruguza Makarantar Malam Abduljabbar Kano

Dazu dazun nan gwamnatin jahar Kanon ta tura jami'an ma'aikatar lura da tsarin filaye in da ta ruguza makarantar Malam Abduljabbar. Gwamnatin dai ta taba bayyana cewa filin da ya ke amfani da shi haramtacce ne, in da ta kai ga kwace shi tare da bada umurnin gudanar da wasu muhimman ayukka a wurin. Dangantaka dai ta yi tsami tsakanin gwamnatin jahar Kano da Abduljabbar in da a ranar laraba sakataren watsa labaran gwamnatin jahar, Muhammad Garba ya bayar da sanarwar rufe masallacin Malam Abduljabbar tare da hana masa gudanar da wa'azi baki daya. In da ta ce hakan na da alaka da irin yadda ya ke tunzura jama'a a kalaman da ya ke amfani da su a lokacin da ya ke da'awa.

Gunmen Abducted 11 FAAN Staff In Kaduna

A group of gunmen yesterday attacked the residences of the Federal Airport Authority of Nigeria Kaduna. Reports say gunmen stormed the compound and abducted at least 11 people. Recent reports suggest that the bandits also abducted a staff of  Nigerian Airspace Management Agency NAMA, his wife, a National Meteorological Agency (NIMET) official and his children.Their whereabouts are still unknown. Kidnappings are common in Nigeria today, and almost every morning there are reports of killings or kidnappings for ransom. Last week Nigerian President Muhammadu Buhari vowed to end abduction in Nigeria but for all indications his words were not effective.

The Nigerian Governors Forum Describe The Militant Attack On Benue State Governor As Shocking

The Nigerian Governors Forum (NGF) has described the militant attack on the Benue State governor as "shocking" and "scary".  Governor Samuel Ortom's delegation was attacked by gunmen on Saturday on the Makurdi-Gboko road, when he visited his farm.  In a statement issued by the group's chairman and Ekiti State Governor Kayode Fayemi on Sunday, the NGF congratulated Ortom for the escape from the attack which it said was "scary and offensive".  Inspector General of Police Mohammed Adamu also condemned the attack and ordered that security be beefed up on the governor and an investigation launched.  "The NGF has said in a loud voice that efforts to rehabilitate Benue State will not succeed," the statement said.  "One of the relatives of a former governor of the state was recently killed. This kind of act of violence must be stopped for whatever reason to kill the people of Benue."

Burtaniya Ta Kakabawa Bankunan Rasha da Mahukuntan Kasar Takunkumin Tattalin Arziki Mafi Girma A Tarihi

Getty images Firaministan Burtaniya, Boris Johnson ya sanar da sakawa Rasha takunkumi mafi tsanani a bangaren tattalin arziki da Rasha ta taba gani, tun bayan da ta mamaye Ukraine. Da yake magana a zauren majalisar, firaministan ya ce za a daskarar da duk wasu manyan bankunan kasar Rasha da kuma cire su daga tsarin kudi na Burtaniya.  Har ila yau, za a dakatar da kamfanin jiragen saman Rasha na Aeroflot sauka a kasar Birtaniya. Mista Johnson ya shaidawa majalisar dokokin kasar a yammacin ranar almais din makon nan cewa, shugaban kasar Rasha Vladimir Putin "mai cin zali ne mai zubar da jini, don haka zai yabawa aya zakinta".

Yahaya Bello Ya Caccaki Buhari

Da ya ke jawabi a lokacin da ake gudanar da shirin zaben fitar da gwani, gwamnan jahar Kogi Yahaya Bello ya nemi a zabe shi domin ya magance matsalar tsaro da karancin ilmi da ake fama da su yanzu haka a Najeriya. Ya ce, "akwai takaici ace wai yanzu malaman jami'a suna ci gaba da yajin aiki, dalibai na zaune a gida kuma an kasa magance wannan matsala mai saukin magancewa". Yahaya Bello wanda ya ce ba zai jaye ma kowa a neman tikitin shugaban kasa, ya kara da cewa shi matashi ne kuma matasa ya kamata a ba dama su mulki kasar nan ba tsofaffi da suka gaji ba. Ya yabawa shugaba Buhari akan saka hannu a kan dokar ba matasa damar tsayawa takara, in da ya ce abu ne mai kyau. Ya yi kira ga mata da sauran 'yan Najeriya da ya ce ana zalunta da su zabe shi. Dan takarar ya ce "yanzu haka babu tsaro ko kadan kuma an kyale, ana kashe mutane ana kona mu su dukiya kuma ana kallo an zura ido".

Binani Ta Zama Mace Ta Farko Da AKa Zaɓa Gwamna A Najeriya

A wani abinda ba saban ba, Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta bayyana Sanata Aisha Dahiru, wacce aka fi sani da Binani a matsayin wadda ta lashe zaɓen gwamnan jahar Adamawa. Kwamishinan zaɓen jahar Adamawa, Farfesa Hudu Yunus Ari, ya ayyana Binani a matsayin wadda ta lashe zaɓen ana tsakiyar tattara sakamakon zaɓen. An bayyana sakamako daga ƙananan hukumomi 10 cikin 20 yayin da aka dage ci gaba da bayyana sakamakon zaɓen har zuwa karfe 11 na safe. Sai dai Ari ya sanar da sakamakon ƙarshe awa ɗaya kafin lokacin da aka tsara. Gwamnan jahar Ahmadu Fintiri na jam'iyyar PDP ne ke kan gaba kafin a bayyana hakan. Wasu magoya bayan jam’iyyar PDP a zauren sun nuna rashin amincewarsu da dalilin da ya sa kwamishinan zaɓe ya sanar da sakamakon maimakon baturen tattara sakamakon zaɓe a al'adance.