Skip to main content

Patience Jonathan Na Cikin Tsaka Mai Wuya

 

Mai shari’a T.G Ringim na babbar kotun tarayya da ke Legas ya tsayar da ranar 7 ga watan Oktoba, 2021, don sauraren karar da ke neman a kwace dala mikiyan 5.78 da wasu karin dala biiyan N2.4 da ke da nasaba da uwargidan tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan.

A ranar 26 ga watan  Afrilun shekarar 2017, mai shari'a Mojisola Olatoregun ta bayar da umarnin a kwace kudaden na wani dan lokaci bayan da Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta ce suna da alaka da zambar karkatar da kudade.

Hasalima, baya ga wani asusun Patience na sirri mai kimanin dala miliyan 5.78, alkalin ya kuma daskarar da wasu asusun da ke da nasaba da ita ciki har da wani asusun da ta ke a bankin Ecobank tare da ragowar wasu naira biliyan 2.4 da aka bude da sunan kamfunnan La Wari Furniture da Bath Limited.

Amma kokarin tabbatar da umurnin ya gamu da cikas kasancewar lauyan Patience, Ifedayo Adedipe (SAN) da Cif Mike Ozekhome (SAN), lauya ma kare kamfunnan La Wari Furniture da Bath Limited, sun nuna turjiya kan amincewa da shi.

Daga baya lauyoyin biyu sun daukaka kara, in da suke neman ta yi watsi da umarnin kwace kayayyakin na wani dan lokaci tare da kwato kudaden amma Kotun Kolin ta goyi bayan umarnin karamar kotun.

Duk da haka, a tsakiyar lokacin da aka kammala sauraren karar kan kudaden da aka ambata, mai shari'a Olatoregun ya yi ritaya daga daga muminsa a shekarar 2019.

Wannan lamarin ya tilasta wa Alkalin Kotun da ya sake tura batun zuwa ga Mai shari’a Chuka Obiozor don ya saurari hukuncin amma bai saurari karar ba kafin a tura shi Benin.

 A ci gaba da shari’ar a ranar Litinin, Lauyan EFCC, Rotimi Oyedepo, ya yi wa Mai Shari’a Ringim bayanin yadda lamarin ya ke, yayin da lauya mai kare Patience ya sanar da alkalin cewa an dage shari’ar don neman karin bayani saboda ta zo ne a karon farko a gabansa.

Lauyan kamfanonin a nasa bangaren ya bukaci kotun da ta dage shari’ar inda ya ke cewa ta dawo sabuwa fil kuma yana da niyyar shigar da takardar neman kalubalantar gaba dayan yadd aka gudanar da shari’ar.

Ya kuma bukaci kotun da ta ba da dogon lokaci don ba shi damar gabatar da takardar neman hakan.

Da yake amsawa, Oyedepo ya ki amincewa da bukatar sannan ya roki kotun da kar ta bayar da irin wannan a bisa hujjar cewa akwai wani tsari da aka shimfida a Sashe na 17 na Dokar Hukumar Yaki da Almubazzaranci da Dukiyar Jama'a da Sauran Laifuka, wadanda EFCC ta bi diddigi ya zuwa matakin da y sahalewa kotu damar kwace kudaden.

A kokacin zaman kotun Mai Shari'a Ringim ya bayyana cewa shari'ar na da matukar muhimmanci, babu wani mataki da zai iya kakubalantar ta 

 Ya ce, “A ra’ayina na tawali’u, akwai hanyar da za a bi  wajen daukan matakin kalubalantar hukunci ba lallai sai an dage shari'ar ba, wanda a wannan matsayi da aka kai kotu ba ta da qani hurumi na dage shari'ara

 “Amma, kuma kotun ba za ta hana bukatar ba, sakamakon haka, an umarci wanda ake kara na biyu da ya gabatar da bukatar, idan akwai, a cikin kwanaki 14 daga yau, kuma mai shigar da karar zai sami mako guda ya amsa.  Za a saurare shi tare da aiwatar da kudirin kwace kudaden, wanda kuma zai iya zama mataji na karshe.”in ji mai shari'a Ringim.

Mai shari'a Ringim ya dage zaman shari’ar har zuwa ranar 7 ga watan Oktoba, 2021.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

NDE Commences Sustainable Training and Loan Disbursement To 100 Youths in Sokoto

The National Directorate of Employment (NDE) has commenced Sustainable Agricultural Development Scheme (SADTS) and loand disbursement to 100 youths in Sokoto. Director-General of NDE, Malam Abubakar Fikpo, disclosed this on Tuesday in Sokoto during the orientation of agricultural loans disbursement held at Shamsuddeen Plaza. Fikpo represented by the Sokoto State NDE Coordinator Mrs Eunice J. Danmallam, said beneficiaries are entitled to N100,000 each at 9 per cent interest rate. He said the beneficiaries were captured under the Agricultural Enhancement Scheme (AES) and Community-Based Agricultural Empowerment Scheme (CBAES). He added they were also under Graduate Agricultural Empowerment Scheme (GAES) and Sustainable Agricultural Development and Empowerment Scheme (SADES). Fikpo said that six months moratorium was given after which  beneficiaries were expected to repay the loan in installments over a period of three years. Dan Mallam expressed gr...

The Nigerian Governors Forum Describe The Militant Attack On Benue State Governor As Shocking

The Nigerian Governors Forum (NGF) has described the militant attack on the Benue State governor as "shocking" and "scary".  Governor Samuel Ortom's delegation was attacked by gunmen on Saturday on the Makurdi-Gboko road, when he visited his farm.  In a statement issued by the group's chairman and Ekiti State Governor Kayode Fayemi on Sunday, the NGF congratulated Ortom for the escape from the attack which it said was "scary and offensive".  Inspector General of Police Mohammed Adamu also condemned the attack and ordered that security be beefed up on the governor and an investigation launched.  "The NGF has said in a loud voice that efforts to rehabilitate Benue State will not succeed," the statement said.  "One of the relatives of a former governor of the state was recently killed. This kind of act of violence must be stopped for whatever reason to kill the people of Benue."