Skip to main content

DA DUMI-DUMI 'Yan Majalisar Amurka Sun Soma Zama Don Tsige Trump

'Yan majalisar dokokin Amurka sun soma wani zama na musamman yanzu haka, don shirin tsige shugaba Donald Trump, ana sauran kwanaki 9 kacal a rantsar da zababben shugaban kasar Joe Biden.
Kakakin majalisar dattawan kasar Nancy Pelosi a wata hira da tashar talabijin ta NBC, ta ce, "Mista Trump zai fuskanci zahiri ta hanyar girbar abinda ya shuka". Ta ce za su nemi mataimakinsa Mike Pence ya aminta tare da sa hannu akan kudurin dokar da zai nuna amincewa da cewa shugaba Trump bai dace ya shugabanci kasar ba, ko kuma idan har hakan ta ci tura, su soma jefa kuri'ar amincewa da tsige shi a tsakiyar makon nan.
Idan har hakan ta tabbata wannan ya nuna Trump ne shugaban Amurka na farko da aka taba tsigewa har sau biyu. Kuma hakan zai bata ma sa suna da makomar siyasa nan gaba.
Masana shari'a na ganin bayan tsige shi, zai iya fuskantar tuhuma akan zargin ingiza magoya bayansa su kai hari da zanga-zanga a majalisar dokokin kasar, domin hana amincewa da zaben Joe Biden, abinda kuma shi ne irin sa na farko a tarihin kasar.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Da Dumi Dumi An Ceto Yaran Da Aka Sace A Katsina

Sakataren gwamnatin jahar Katsina Alhaji Mustapha Inuwa ya fitar da sanarwar cewa an samu nasarar ceto daliban nan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su daga makarantar kwanan ta Kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina. Ya ce an ceto yaran su 340, kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta isowa jahar daga Tsafen jahar Zamfara. Ana sa ran gobe jumu'a za su gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kafin daga bisani a sada su da iyayensu. Sauran bayani zai zo nan gaba.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey