Skip to main content

An Rantsar Da Shugaba Joe Biden

An rantsar da shugaban Amurka na 46 Joe R. Biden tare da mataimakiyarsa Kamala Harris.
Shugaba Biden ya nemi goyon bayan Amurkawa wajen samar da hadin kan kasa.
"Ina neman hadin kan ku wajen ci gaba da ginin dimukuradiyarmu mai shekaru fiye da dari biyu ta ci gaba", in ji Biden.
Ya kara da cewa, "Fatan da na sa gaba idan na shiga ofis, shine tabbatar da Amurka ta dore a yadda a ka santa, da inganta huldar dangantaka tsakanimu da waje, yaki da korona hadi da tabbatar da Amurka ta ci gaba da zama dunkulalliyar kasa".
Shahararriyar mawakiyar nan, Lady Gaga ce ta rera taken kasar, haka ma mawakiya Jennifer Lopez ta nishandantar da mahalarta bukin.
An dai gudanar da bukin cikin tsauraran matakan tsaro.
Tun da safiyar yau tsohon shugaban Amurka Donald Trump ya bar fadar White House cikin wani jirgi mai saukar ungulu in da ya nufi jahar Florida. A can zai yi jawabin shirin kafa sabuwar jam'iyarsa da ya ce za ta samarwa Amurka makoma kasancewar manyan shugabannin jam'iyar Republican na ta nesanta kan su da shi.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Da Dumi Dumi An Ceto Yaran Da Aka Sace A Katsina

Sakataren gwamnatin jahar Katsina Alhaji Mustapha Inuwa ya fitar da sanarwar cewa an samu nasarar ceto daliban nan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su daga makarantar kwanan ta Kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina. Ya ce an ceto yaran su 340, kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta isowa jahar daga Tsafen jahar Zamfara. Ana sa ran gobe jumu'a za su gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kafin daga bisani a sada su da iyayensu. Sauran bayani zai zo nan gaba.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey