Skip to main content

Posts

NDE Commences Sustainable Training and Loan Disbursement To 100 Youths in Sokoto

The National Directorate of Employment (NDE) has commenced Sustainable Agricultural Development Scheme (SADTS) and loand disbursement to 100 youths in Sokoto. Director-General of NDE, Malam Abubakar Fikpo, disclosed this on Tuesday in Sokoto during the orientation of agricultural loans disbursement held at Shamsuddeen Plaza. Fikpo represented by the Sokoto State NDE Coordinator Mrs Eunice J. Danmallam, said beneficiaries are entitled to N100,000 each at 9 per cent interest rate. He said the beneficiaries were captured under the Agricultural Enhancement Scheme (AES) and Community-Based Agricultural Empowerment Scheme (CBAES). He added they were also under Graduate Agricultural Empowerment Scheme (GAES) and Sustainable Agricultural Development and Empowerment Scheme (SADES). Fikpo said that six months moratorium was given after which  beneficiaries were expected to repay the loan in installments over a period of three years. Dan Mallam expressed gr...

Osinbajo Ya Fito Takarar Shugaban Kasa

A jiya ne mataimakin shugaban Najeriya, Farfesa Yemi Osinbajo ya bayyana aniyarsa ta tsaya takarar shugaban kasar Najeriya a 2023. Ya fadi hakan ne a lokacin wani kwarya-kwaryar buda baki da ya halarta tare da wasu gwamnonin jam'iyyar APC da suka hada da na jahar Kebi Abubakar Atiku Bagudo da na Kaduna Malam Nasiru El-Rufa'i da sauran su. A yau litinin dai ne Osinbajo zai sanar da wannan kudiri nasa a dokance, ta wani jawabi da za a yada ta bidiyo. Idan ana iya tunawa dai watanni biyu da suka gabata mataimakin shugaban Najeriyar ya ce ya sanar da shugaban kasa Muhammadu Buhari wannan manufa tasa. Kafin bayyana wannan bukata, tuni dai wasu suka fito suka bayyana bukatar tsayawa takarar kujerar shugaban kasa karkashin jam'iyyar APC da suka hada da tsohon gwamnan jahar Legas, Bola Ahmed Tinubu da gwamnan jahar Kogi Yahaya Bello da Rochas Okorocha da kuma kwanan nan ministan suhuri kuma tsohon gwamnan jahar Ribas, Rotimi Amechi da sauran su.

An Ga Watan Ramadan A Najeriya

An samu ganin jinjirin watan Ramadan a Najeriya a yau kamar yadda Mai Alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Sa'ad Abubakar na Uku ya bayar da sanarwa. An ga watan a jahohin Sokoto da Kano da Katsina da Filato da Adamawa da sauran jahohi n Najeriya. Gobe asabar 2 ga watan Afirilu 2022 za ta zama 2 ga watan Ramadan 1443.

An Ga Watan Ramadan A Saudiyya

An ga jinjirin watan Ramadan a wurare da dama a kasar Saudiyya. Gobe asabar 2 ga Afrilu 2022 za ta zama 1 ga watan Ramadan 1443.

Zamu Yaki 'Yanta'adda Da Kanmu - El-Rufa'i

Cikin hushi gwamnan jahar Kaduna Malam Nasiru El-Rufa'i ya bayyana cewa idan gwamnatin tarayya ta kasa kare al'umma daga harin 'yan bindiga to fa za su hada kai su kare jama'arsu, ko da kuwa ta kama su dauko sojojin haya daga ketare. Ya fadi hakan a wata hira da BBC ta yi da shi, in da ya ce dukan hare-haren da ake kai wa jama'a gamnatin tarayya na sane kuma sun san mazaunar 'yan ta'addan. Ya kara da cewa da jimawa shi kan sa ya sha ba shugaban kasa shawara akan matakan da ya kamata a dauka na yakar masu tayar da tarzoma da kisan jama'a a jahohin arewa maso gabas da arewa maso yamma amma sai a ka yi biris da shawarar da ya bayar.

Kwankwaso Ya Fice Daga PDP

Getty images Labarin da ke shigo muna yanzu haka sun tabbatar da tsohon gwamnan jahar Kano, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya fitar da sanarwar ficewa daga jam'iyyar ta PDP zuwa sabuwar jam'iyyar NNPP, jim kadan bayan da kotu ta bayar da umurnin dakatar da helkwatar jam'iyyar PDP ta kasa daga rusa membobin kwamitin zartaswar jam'iyyar reshen jahar Kano.

An Zabi Abdullahi Adamu Shugaban Jam'iyyar APC

Getty images Jam'iyyar APC ta cimma matsayar zabar tsohon gwamnan jahar Nasarawa, Alhaji Abdullahi Adamu, a matsayin sabon shugabanta. Kimanin 'yan takara shida ne suka janye daga neman mukamin, da suka hada da tsohon gwamnan jahar Nasarawa Alhaji Tanko Almakura da tsohon gwamnan jahar Borno Ali Modou Sheriff da tsohon gwamnan jahar Zamfara Abdul'aziz Yari Abubakar Mafara da sauran su. Tun da farko dai an bayyana Abdullahi Adamu a matsayin dan takarar da shugaban kasa Muhammadu Buhari ke marawa baya.