Skip to main content

Putin Ya Ziyarci Sansanin Soja Na Kherson Da Ke Ukraine

Shugaban Rasha Vladimir Putin ya ziyarci yankunan Ukraine da aka mamaye a karo na biyu tun bayan ƙaddamar da wani gagarumin farmaki, kamar yadda fada Kremlin ta sanar a yau Talata.
Putin ya ziyarci hedkwatar soji a yankin Kherson na kudancin ƙasar Ukraine da kuma hedkwatar tsaron Rasha da ke yankin Luhansk.
Tafiyar ta zo ne a daidai lokacin da Rasha ke ci gaba da kai hare-hare a gabashin Ukraine.
Jaridar ƙasar Rasha taThe Moscow Times https://www.themoscowtimes.com/2023/04/18/putin-visits-occupied-ukraine-territories-a80862 ta bayyana cewa Fadar Kremlin ba ta bayyana takamaiman lokacin da tafiyar ta gudana ba kuma hotunan ziyarar biyu sun nuna Putin sanye da tufafi daban-daban.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Da Dumi Dumi An Ceto Yaran Da Aka Sace A Katsina

Sakataren gwamnatin jahar Katsina Alhaji Mustapha Inuwa ya fitar da sanarwar cewa an samu nasarar ceto daliban nan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su daga makarantar kwanan ta Kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina. Ya ce an ceto yaran su 340, kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta isowa jahar daga Tsafen jahar Zamfara. Ana sa ran gobe jumu'a za su gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kafin daga bisani a sada su da iyayensu. Sauran bayani zai zo nan gaba.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey