Skip to main content

Da Dumi Dumi Shugaba Idris Deby Ya Mutu

Shugaban kasar Chadi Idris Deby ya mutu a lokacin da ya jagoranci dakarun tsaron kasar a karshen mako, wadanda ke fafatawa da 'yan tawaye akan iyakar kasar da Libya da ke arewacin kasar.
Shugaba Deby wanda ake hasashen zai iya lashe babban zaben kasar da kashi 80 bayan ya nemi tsayawa takara a karo na shida.
Yanzu dai dakarun sojin kasar sun rosa rusa majalisar dokokin tare da bayar da sanarwar rike madafun iko na tsawon watanni 18 kafin gudanar da sabon zabe.
Idris Deby ya soma mulkin kasar Chadi a 1990 bayan ya yiwa gwamnatin tsohon shugaban kasar, Hissene Habry juyin mulki, in da kuma ya kwashe shekaru 30 akan karagar mulkin kasa ta Chadi.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey