Skip to main content

Jami’an Hukumar Binciken Manyan Laifuka ta Amurka FBI Sun Kai Samame Gidan Dold Trump

 

Tsohon shugaban ƙasar Amurka Donald Trump ya bayyana a cikin wata sanarwa da ya fitar cewa tawagar jami’an hukumar sun mamaye gidansa na alfarma da aka fi sani da suna Ma-a-Lago da ke a gaɓar tekun jahar Fulorida.

Rahotanni sun nunar da cewa samamen na da nasaba da wani bincike da ake kan gudanarwa da ke zargin Mista Trump da riƙe wasu muhimman takardun gwamanati tun bayan saukar sa daga mulki.

Sai dai Mista Trump ya bayyana wannan mataki da kutsen da ya saɓawa doka, “Babu wani abu makamancin wannan da ya taɓa faruwa da Shugaban Amurka a tarihance”.

Sashen adana bayanan gwamnatin Amurka ya sanar tun a farko cewa, Mista Trump bai miƙa wasu muhimman takardu ba da suka haɗa da wasiƙu da ya zama wajibi duk shugaban ƙasa mai barin gado ya hannunta bayan barin sa mulki.

Jami’an ofishin sun ce sun gano manyan akwatuna 15 a gidan waɗanda ke ɗauke da muhimman takardun. Daga baya sashen adana bayanan ya shaidawa majalisar dokokin Amurka cewa kowace akwati da aka gano an yi mata alama da rubutu da aka bayyana “Bayanan Asirin Ƙasa”; in da aka yi nasarar ƙwace su a lokacin samamen.

Wannan matakin dai ya jawo cece-ku-ce a faɗin ƙasar in da ɗaruruwan magoya bayansa suka taru a gaban gidansa na alfarma na Mar-a-Lago suna ɗaga totoci tare da nuna adawa da abinda suka kira bita-da-ƙulli.

Ɗan majalisar wakilan jami’iyyar Republican maidawa, Kevin MacCarthy, ya nunar da matakin a matsayin wanda ya saɓawa dokokin ƙasara, “Mun gaji da haka. Sashen Dokokin ƙasa ya wuce gona da iri, in da ba za a iya ci gaba da jure amfani da ƙarfin mulki ba wajen bibiyar ‘yanadawa”.

A cewar tshon shugana ƙasar wannan ba kome ba ne face yunƙurin hana shi tsayawa takarar shugaban ƙasa nan gaba, abinda kuma ya ce ba za ta saɓu ba.

 

 

 

 

 

Comments

Popular posts from this blog

Iran seeks talks with us after threat of attack – Trump

U.S. President Donald Trump has said that Iranian authorities have contacted the United States to seek talks, following his threat to take military action over the killing of protesters in the country. Trump made the statement while speaking to journalists, saying that a meeting between the two sides has already been planned, but that the United States might take some action before the meeting takes place. Meanwhile, a human rights organization in Iran says it has confirmed the deaths of nearly 500 people since the outbreak of the protests. Likewise, some circulating video clips show a site outside Iran where bodies are being kept, with people going there to search for the remains of their relatives who have gone missing.

Murtala Abdulkadir Dan Iya Gambun Sakkwatawa

Alhaji Murtala Abdulkadir Dan Iya ya shahara wajen ayyukan jinƙai a Jihar Sokoto tsawon  shekarun ya zuwa yanzu. Alhaji Murtala Abdulkadir Dan Iya shugaban Hukumar Bayar Da Tallafin Ƙaro Karatu ta Jihar Sokoto  A tattaunawar da jaridar Tantabara News ta yi da Nura Muhammad Chiso, wanda ke jagorancin daya daga cikin ƙungiyoyin Alhaji Murtala Abdulkadir Dan Iya, mai suna da ke bayar da tallafi da wayar da kan al'umma a jihar ta Sokoto, ya bayyana tarin manyan tallafan da wannan shahararren ɗan kasuwa, kuma ɗan siyasa ya yi wa dubban mutane mabukata a jihar, lamarin da ya ƙara ɗaukaka darajar sunansa a cikin jihar da ma wajenta. N ura Muhammad Chiso  Nura Muhammad Chiso ya ce, "wannan aikin alheri na shugaban Hukumar Bayar Da Tallafin Ƙaro Karatu ta Jihar Sokoto, wani babban aikin alheri ne da ya gane dubban jama'a talakawa har hakan ya sa suke kiran sa da gambun Sakkwatawa saboda faranta musu rai da yake yi". Ga wa...

WHEN LIES GO VIRAL: DEFENDING TRUTH IN NIGERIA AND WEST AFRICA’S DIGITAL PUBLIC SPHERES

Across Nigeria and West Africa, digital technology has reshaped how citizens engage with information, governance, and public debate. Mobile phones and social media platforms have become dominant sources of news, especially for young people and communities with limited access to traditional media. While this transformation has expanded civic participation and freedom of expression, it has also intensified the spread of misinformation, posing serious risks to democracy, public health, and social cohesion. Misinformation is no longer a marginal problem. It is a structural challenge that affects elections, security, development communication, and trust in public institutions. Addressing it requires coordinated action that combines ethical journalism, media literacy, platform accountability, and evidence based policy responses. THE DIGITAL INFORMATION LANDSCAPE IN NIGERIA AND WEST AFRICA Nigeria is Africa’s most populous country and one of its most digitally active societies. So...