Skip to main content

Jami’an Hukumar Binciken Manyan Laifuka ta Amurka FBI Sun Kai Samame Gidan Dold Trump

 

Tsohon shugaban ƙasar Amurka Donald Trump ya bayyana a cikin wata sanarwa da ya fitar cewa tawagar jami’an hukumar sun mamaye gidansa na alfarma da aka fi sani da suna Ma-a-Lago da ke a gaɓar tekun jahar Fulorida.

Rahotanni sun nunar da cewa samamen na da nasaba da wani bincike da ake kan gudanarwa da ke zargin Mista Trump da riƙe wasu muhimman takardun gwamanati tun bayan saukar sa daga mulki.

Sai dai Mista Trump ya bayyana wannan mataki da kutsen da ya saɓawa doka, “Babu wani abu makamancin wannan da ya taɓa faruwa da Shugaban Amurka a tarihance”.

Sashen adana bayanan gwamnatin Amurka ya sanar tun a farko cewa, Mista Trump bai miƙa wasu muhimman takardu ba da suka haɗa da wasiƙu da ya zama wajibi duk shugaban ƙasa mai barin gado ya hannunta bayan barin sa mulki.

Jami’an ofishin sun ce sun gano manyan akwatuna 15 a gidan waɗanda ke ɗauke da muhimman takardun. Daga baya sashen adana bayanan ya shaidawa majalisar dokokin Amurka cewa kowace akwati da aka gano an yi mata alama da rubutu da aka bayyana “Bayanan Asirin Ƙasa”; in da aka yi nasarar ƙwace su a lokacin samamen.

Wannan matakin dai ya jawo cece-ku-ce a faɗin ƙasar in da ɗaruruwan magoya bayansa suka taru a gaban gidansa na alfarma na Mar-a-Lago suna ɗaga totoci tare da nuna adawa da abinda suka kira bita-da-ƙulli.

Ɗan majalisar wakilan jami’iyyar Republican maidawa, Kevin MacCarthy, ya nunar da matakin a matsayin wanda ya saɓawa dokokin ƙasara, “Mun gaji da haka. Sashen Dokokin ƙasa ya wuce gona da iri, in da ba za a iya ci gaba da jure amfani da ƙarfin mulki ba wajen bibiyar ‘yanadawa”.

A cewar tshon shugana ƙasar wannan ba kome ba ne face yunƙurin hana shi tsayawa takarar shugaban ƙasa nan gaba, abinda kuma ya ce ba za ta saɓu ba.

 

 

 

 

 

Comments

Wadanda aka fi karantawa

Wanene Ɗan Jarida?

Ɗan jarida mutum ne kamar kowa, sai dai tunaninsa da manufofinsa kan tafi daidai ne kawai da ra'ayin MASU SAURARO ta fuskokin da suka shafi aikinsa. Ya zama mai wakiltar waɗanda ba su da baki ne ko kafafuwan zuwa, kuma idanuwan talakawa a kowane lokaci. Idan ka nuna ma sa launi shuɗi, ƙoƙarin ya ke ya tabbatar da launin nan shuɗi ne ziryan ko yana da garwaye? Idan ka ce ma sa labarin abu kaza ya faru, ba zai ce a'a ba kuma ba zai ce eh ba, aikinsa shi ne TABBATARWA . Idan mai sauraro namiji ne ko mace ko mai ra'ayin wani addini ko akida ko mai kuɗi ko talaka, ɗan jarida kan GIRMAMA kowa, kuma zai ɗauki kowa a matsayin DAIDAI ta fuskar ba su damar bayyana ra'ayoyinsu. Ɗan jarida kan tafi da zamani, ya kuma rungumi fasahar da ƘIRƘIRA ta kawo domin tafiya daidai lokaci. A kowace marra GASKIYA ita ce madogarar ɗan jarida, kuma wannan kan ƙara sa masu sauraro su amince da shi. Amma kuma, dole ne ɗan jarida ya zama MAI IKON KANSA , ba zai yi ma kowa alfarma b...

Binani Na Neman Kotu Ta Tabbatar Da Ita Wadda Ta Lashe Zaɓen Adamawa

Magoya bayan jam’iyyar PDP a jihar Adamawa a ranar Litinin sun fito kan tituna domin nuna adawa da ayyana Sanata Aishatu Dahiru Binani a matsayin wadda ta lashe zaben gwamnan Adamawa. Sai dai ita Binani ta buƙaci wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta dakatar da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta kasa (INEC) daga sauya matakin da aka ɗauka na ayyana ta da a ka yi a matsayin wadda ta lashe zaɓen.  A wata buƙata da ta shigar a ranar Litinin, mai neman izinin kotun ya nemi izinin kotun ta ba ta damar shigar da buƙatar neman umarnin haramtawa INEC daga ɗaukar duk wani mataki na watsi da sanarwar da aka yi a ranar 16 ga Afrilu da Kwamishinan zaɓen jahar, Barista Hudu Ari ya ayyana ta a matsayin wadda ta samu ƙuri'u mafifi rinjaye kuma ta lashe zaɓen alhali ba a kammala tattara sakamakon zaɓen gaba ɗaya ba. Ta kuma nemi a ba da umarnin hana hukumar zabe ta INEC, da wakilinta nadawa ko kuma duk wanda ke wakiltarta daukar wasu matakai na bayyana wanda ya lashe zaben gwamna da ak...