Skip to main content

Gwamna Tambuwal Ya Umurci Malaman Jami'ar Sokoto Su Koma Aiki

Gwamnan jahar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal, ya umurci Malaman Jami’ar  Jahar Sokoto da su koma bakin aiki ba da bata lokaci ba,bayan kwashe wata shida jami’ar na rufe  sakamakon yajin aikin Kungiyar Malamn Jami’a (ASUU).
Wannan mataki na kama da bayar da umurnin nan take in da ya nuna matukar bacin ransa yadda malaman ke ci gaba da kauracewa wuraren aikinsu da zimmar bin umurnin kungiyar ta ASUU.
Ya kuma nunar da cewa babu wani hakki da malaman jami’ar Jahar Sokoto ke bin gwamnatinsa kama daga albashi ya zuwa sauran bukatu da bai yi mu su ba.
Ya bayyana cewa babu wata matsala a duniya da ta gagari tattaunawar da za ta kai ga cimma maslaha, kuma ya zama wajibi a fito da matakin da zai iya zama kandagarki ga duk wani abu da ke haifar da yajin aiki a Najeriya.
“Bai kamata ku biyewa uwar kungiya ta ASUU ba, saboda matsalolinsu ba su shafe ku ba. Kuna cutar da dalibanku ne kawai, kuma wannan biyayyar da kuke  ci gaba da yi na da matukar muni da nakasu ga makomar ilmi; ina mai ba ku umurnin nan take ku koma bakin aiki ba tare da wani bata lokaci ba”, in ji gwamna Tambuwal.
Gwamnan na wadannan kalaman ne lokacin da ya karbi rahoton binciken da kwamitin da gwamnatin jahar Sokoto ta kafa karkashin jagorancin Injiniya Abdullahin Bakale, da ya gudanar da bincike dangane da tarzomar daliban Kwalejin Ilmi ta Shehu Shagari da ta yi sanadiyyar mutuwar wata Daliba mai suna Deborah Yakubu, har  ya jawo aka rufe kwalejin.
Wannan umurnin gwamnatin jahar Sokoto na zuwa ne kwanaki kadan da kungiyar ta ASUU ta fitar da sanarwar tsawaita yajin aikin da ta ke yi da makonni hudu, lura da cewa har yanzu gwamnatin Najeriya ba ta gaji da zaman dalibai a gida ba.
An soma yajin aikin tun ranar 14 ga watan Febarairun bana, a bisa dalilin kasa cimma matsaya tsakanin Gwamnatin Tarayya da Kungiyar Malaman Jami’a na cika alkawurran da gwamnati ta dauka na inganta rayuwar malaman ciki har da maganar shigar da malaman cikin tsarin albashin bai daya da ka fi sani da IPPIS.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

NDE Commences Sustainable Training and Loan Disbursement To 100 Youths in Sokoto

The National Directorate of Employment (NDE) has commenced Sustainable Agricultural Development Scheme (SADTS) and loand disbursement to 100 youths in Sokoto. Director-General of NDE, Malam Abubakar Fikpo, disclosed this on Tuesday in Sokoto during the orientation of agricultural loans disbursement held at Shamsuddeen Plaza. Fikpo represented by the Sokoto State NDE Coordinator Mrs Eunice J. Danmallam, said beneficiaries are entitled to N100,000 each at 9 per cent interest rate. He said the beneficiaries were captured under the Agricultural Enhancement Scheme (AES) and Community-Based Agricultural Empowerment Scheme (CBAES). He added they were also under Graduate Agricultural Empowerment Scheme (GAES) and Sustainable Agricultural Development and Empowerment Scheme (SADES). Fikpo said that six months moratorium was given after which  beneficiaries were expected to repay the loan in installments over a period of three years. Dan Mallam expressed gr...

The Nigerian Governors Forum Describe The Militant Attack On Benue State Governor As Shocking

The Nigerian Governors Forum (NGF) has described the militant attack on the Benue State governor as "shocking" and "scary".  Governor Samuel Ortom's delegation was attacked by gunmen on Saturday on the Makurdi-Gboko road, when he visited his farm.  In a statement issued by the group's chairman and Ekiti State Governor Kayode Fayemi on Sunday, the NGF congratulated Ortom for the escape from the attack which it said was "scary and offensive".  Inspector General of Police Mohammed Adamu also condemned the attack and ordered that security be beefed up on the governor and an investigation launched.  "The NGF has said in a loud voice that efforts to rehabilitate Benue State will not succeed," the statement said.  "One of the relatives of a former governor of the state was recently killed. This kind of act of violence must be stopped for whatever reason to kill the people of Benue."