Skip to main content

Zabar Alhaji Sa'idu Umar Ubandoma Matsayin Dan Takarar Gwamnan Jahar Sokoto A Jam'iyyar PDP Ya Bar Baya Da Kura


Bayan da gwamnan jahar Sokoto Aminu Waziri Tambuwal ya jagoranci zaman sulhu domin tsayar da dan takarar gwamna a karkashin jam'iyyar PDP tare da zabar Alhaji Sa'idu Umar Ubandoma, hakan ya haifar da cece-kuce tsakanin jama'a.

Daga cikin jerin 'yan takarar da suka nemi kujerar akwai mataimakin gwamnan jahar Sokoto, Alhaji Maniru Muhammed Daniya da kwamishin muhalli na jahar Sokoto, Alhaji Sagir Attahiru Bafarawa da tsohon sakataren gwamnatin jahar Sokoto, Alhaji Sa'idu Umar Ubandoma da kuma tsohon mataimakin gwamnan jahar Sokoto Alhaji Muktari Shagari.

Bayan zama da gwaman Aminu Waziri Tambuwal ya yi da dukan su a dakin taro na kasa da kasa da ke Kasarawa, daga karshe gwamnan ya tabbatar da Sa'idu Umar Ubandoma a matsayin wanda zai yi ma jam'iyyar PDP takarar gwamna a 2023.

Rahotannin da ke shigo muna yanzu haka sun tabbatar da cewa shi ma daya daga 'yan takarar da bai yi nasara ba, Alhaji Muntari Shagari ya fice daga jam'iyar ta PDP sai dai bai bayyana in da zai koma ba, kamar yadda ya wallafa a shafinsa na Facebook cewa, "Ina son sanar da magoya bayana cewa daga yau na fice daga jam'iyar PDP domin kyakkyawar manufa. Zan sanar da matakin da zan dauka nan gaba."
Sabuwar zanga-zangar da aka soma ta karade wurare da dama a Sokoto, in da su ke bayyana rashin amincewa da zabin da suka ta'allaka ga gwamna Tambuwal tare da yin kalamai masu zafi, kamar yadda wani shi ma mai suna Shamsu Ibrahim ya wallafa bidiyon a shafinsa na Facebook.
Wani shi ma mai suna Zaharaddeen Photos Hamma'ali ya wallafa bidiyo makamancin wannan, in da ake jin wata murya na cewa za su bar Tambuwal su bi Atiku.
Ku dannan kafar da ke kasa don ganin bidiyon biyu:






Comments

Wadanda aka fi karantawa

NDE Commences Sustainable Training and Loan Disbursement To 100 Youths in Sokoto

The National Directorate of Employment (NDE) has commenced Sustainable Agricultural Development Scheme (SADTS) and loand disbursement to 100 youths in Sokoto. Director-General of NDE, Malam Abubakar Fikpo, disclosed this on Tuesday in Sokoto during the orientation of agricultural loans disbursement held at Shamsuddeen Plaza. Fikpo represented by the Sokoto State NDE Coordinator Mrs Eunice J. Danmallam, said beneficiaries are entitled to N100,000 each at 9 per cent interest rate. He said the beneficiaries were captured under the Agricultural Enhancement Scheme (AES) and Community-Based Agricultural Empowerment Scheme (CBAES). He added they were also under Graduate Agricultural Empowerment Scheme (GAES) and Sustainable Agricultural Development and Empowerment Scheme (SADES). Fikpo said that six months moratorium was given after which  beneficiaries were expected to repay the loan in installments over a period of three years. Dan Mallam expressed gr...

The Nigerian Governors Forum Describe The Militant Attack On Benue State Governor As Shocking

The Nigerian Governors Forum (NGF) has described the militant attack on the Benue State governor as "shocking" and "scary".  Governor Samuel Ortom's delegation was attacked by gunmen on Saturday on the Makurdi-Gboko road, when he visited his farm.  In a statement issued by the group's chairman and Ekiti State Governor Kayode Fayemi on Sunday, the NGF congratulated Ortom for the escape from the attack which it said was "scary and offensive".  Inspector General of Police Mohammed Adamu also condemned the attack and ordered that security be beefed up on the governor and an investigation launched.  "The NGF has said in a loud voice that efforts to rehabilitate Benue State will not succeed," the statement said.  "One of the relatives of a former governor of the state was recently killed. This kind of act of violence must be stopped for whatever reason to kill the people of Benue."