Skip to main content

Rasha Na Shirin Kai Ma Amurka Da Kawayenta Hari

Reuters
Rasha ta gargadi kasashen yammacin duniya da cewa za a dauki tsauraran matakin soji kan duk wani hari da za a kai a yankin na Rasha, tana mai zargin Amurka da manyan kawayenta da zagon kasa ga tsaron kasashen Turai ta hanyar tunzura Ukraine a fili ta kai wa Rasha hari.
Yunkurin mamayar da Rasha ta yi a Ukraine a ranar 24 ga watan Fabrairu ya yi sanadin mutuwar dubban mutane, ya raba wasu miliyoyi da matsugunansu, ya kuma haifar da fargabar kazamin fada mafi muni tsakanin Rasha da Amurka, tun bayan rikicin makami mai linzami na Cuba a shekara 1962.
Watanni biyu tun bayan da Rasha ta mamaye Ukraine, a cikin 'yan kwanakin nan Rasha ta ba da rahoton wani jerin hare-haren da sojojin Ukraine suka kai a yankunan Rasha da ke makwabtaka da Ukraine, kuma ta yi gargadin cewa irin wadannan hare-haren na da hadari sosai.
Ukraine ba ta dauki alhakin kai tsaye ba, amma ta ce abubuwan da suka faru na mayar da martani ne, yayin da Rasha ta yi kakkausar suka ga kalaman da kungiyar tsaro ta NATO da Birtaniyya ta yi cewa ya dace Ukraine ta kai hari kan kayan aikin Rasha.
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Rasha Maria Zakharova ta shaidawa manema labarai a birnin Moscow cewa, "A kasashen yammacin duniya, suna kira a fili ga Kyiv da ya kai wa Rasha hari ciki har da amfani da makaman da aka samu daga kasashen NATO."
"Ban baki shawara ki kara gwada hakurin mu ba."
Fadar Kremlin ta ce kasashen Yamma - musamman ma Birtaniya, na yunkurin kai manyan makamai ga Ukraine wanda babbar barazana ce ga tsaron Turai.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Da Dumi Dumi An Ceto Yaran Da Aka Sace A Katsina

Sakataren gwamnatin jahar Katsina Alhaji Mustapha Inuwa ya fitar da sanarwar cewa an samu nasarar ceto daliban nan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su daga makarantar kwanan ta Kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina. Ya ce an ceto yaran su 340, kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta isowa jahar daga Tsafen jahar Zamfara. Ana sa ran gobe jumu'a za su gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kafin daga bisani a sada su da iyayensu. Sauran bayani zai zo nan gaba.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey