Skip to main content

Kalubalen Fassarar Labarai A Rediyo

Fassara dai na nufin juya ma'ana daga wani harshe zuwa wani ba tare da canza sakon asali ba.
Ya zama wajibi mai fassara ya zama mutum mai cikakken hankali, da ya mallaki harsunan da yake fassara daga gare su zuwa gare su.

Abin da ake nufi a nan shi ne cewa dole ne mai yin fassara ya san harsunan da zai yi wa fassara, sannan ya yi musu kyakkyawar fahimta; wato ya san harshen da aka yi magana da shi, sannan da wanda zai juya maganar zuwa cikinsa. Misali, wanda zai riƙa yin fassara daga Ingilishi zuwa Hausa dole ya fahimci harshen Hausar da kuma Ingilishi, fahimta kuma ta haƙiƙa.
Sanin al’adu: Dole ne mai yin fassara ya san al’adun waɗanda zai fassara maganar zuwa harshensu. Misali, idan mai fassara zai yi fassara zuwa harshen Hausa, to dole ya san al’adun Hausawa, sani kuma ba na shanu ba.
Haka kuma, dole ne mai yin fassara ya kasance mai zurfafa bincike a fannonin ilimi dan ya samu isassun kalmomin da za su taimaka masa wajen yin kyakkyawar fassara. Amma idan bai fahimci duka wadannan abubuwan ba, babu shakka zai fada rudani da rikici.

Getty images
Kome Ya Sa Ake Samun Tasgaro A Fassara?
Abubuwa da yawa na taka rawa wajen gurgunta ma'anar labarin da aka fassara. Hasalima idan mai fassara bai nakalci al'ada da harsunan da yake fassara daga gare su zuwa gare su ba. Sanin asali da muhallin kalma wani karfi ne da zai taimaki mafassari gano in da aka dosa.
Kalmar sanadi ko tushe a turance, ta rarrabu zuwa dakuna da yawa kamar, cause da source da origin da genesis da beginning da sauran su, wadanda gaba daya na da kamanceceniya sai dai ya danganta da muhallin da kowacen su ta samu kanta, domin a harshe babu wata kalma da ta ke daidai da wata dari bisa dari. 

Wannan ma ne dalilin da ya sa ake kiran synonyms a matsayin "words which are almost similar or identical in meaning", wato kalmomi masu matukar kama da juna. Ba a ce kalmomi iri daya ba, domin duk abu biyu dole daya ya sabawa daya koda a launi ne.

Kuma sau da yawa mai fassara kan shiga damuwa idan ya kasa fahimtar wannan, har ma ya shiga kokwanton cewa ta ya zai fassara wasu kalmomi musamman wadanda babu takwararsu a harshen da ya ke fassara cikin sa kamar nemo takwarar kalmar pear a harshen Hausa da takwarar kalmar mango.

Abu ne mai sauki fassara mango a matsayin mangoro kasancewar akwai shi a kasar Hausa duk kuwa da cewa bako ne, kuma an Hausance kalmar ne kawai.
Wato dai akwai muhalli ko sarari da aka ba mai yin fassara na Hausance ko baddala zance cikin nasa ba tare da ya jirkita sakon zuwa wani abu daban ba.

Wani abin lura a nan shi ne, dole ne mai fassara ya yi amfani da 'yancin da aka ba shi na nemo dangin kalma ko wadda za ta iya maye gurbinta ko kuma ya yi amfani da bayani. Sai dai wannan ba ya na nufin ka yi fassarar kama karya ko ta 'yan zamani ba, ta yadda mai fassara zai kira miyar kuka da baobab leaves soup. Akwai wani abu da masana harshe ke kira Sahalewar harshe cikin al'ada da Ingilishi kuma Linguistic
Determinism. Wannan tsarin ya tabbatar da cewa kowane harshe makale ya ke da al'adarsa. Misali duk kalmar da ta kebantu ga al'adar wasu jama'a na wata kasa ko nahiya to da wuya kuma wasu jama'ar daban su iya fassara ta a nasu harshe.
Dauki misalin snow, wadda ke ma'anar kankara da ke zuba a lokacin sanyi na shekara-shekara a kasashen Turai da Asiya.

Getty images
Da kuma iceberg wato kankarar da ke saman teku wadda kuma fiye da kashi 7 cikin 10 nata yana kasan ruwan. 

Getty images
Sai kuma ice wato kankara irin wadda kan fado lokacin ruwan sama kuma wadda akan samu a firiji.

Getty images
Duka wadannan nau'i ne na kankara amma kowace da sunanta snow, iceberg da kuma ice.
Dalilin ba su sunaye bamban na da alaka da al'adu da muhallan da suka fito amma mai fassara cikin harshen Hausa babu abinda ya iya face ya kira su da kankara kawai, sai fa idan zai bi da dan bayani don saukakewa mai karatu ko saurare gane bambancinsu.
Idan har mai yin fassara ya mallaki wannan basira cikin aikinsa, to babu shakka zai samu natsuwar isar da sako.

Getty images
Shin me yasa kalmar sanadi ta zama wata mai rudarwa ga masu fassarar labaru a rediyo?
Bari mu mayar da hankali a kan yadda masu fassara labarai a rediyo ke tuya su manta albasa. Ga wani dan misali:
"The flood causes the death of five year old child."

*"Ambaliyar ruwan ta yi sanadin rayuwar yaron dan shekara biyar.
Wannan fassara ba daidai ta ke ba, saboda babu yadda za a yi wani mutum ya iya sanadin rai?

Sanadin abu fa na ma'anar samar da shi ko kirkiro shi.
Dubi wannan jimla kuma:

"Kallau ne ya yi sanadin barin aikin Hankurau!"

A wannan jimla ta sama mun lura an yi amfani da kalmar "sanadi" amma kuma an hada ta da kora.

Idan misali ta koma haka fa?

"Kallau ne yayi sanadin aikin Hankurau"

Kenan a fili ta ke akwai bambanci tsakanin jimlar farko mai dauke da karin kalmar kora da kuma ta biyu mai dauke da kalmar "sanadi kawai.

Misali sanadin aure da sanadin mutuwar aure jimloli ne da suka bambanta ta kowane bangare kuma kishiyoyin juna ne.
Babban kuskure ne ka yi amfani da kalmar "sanadi" ba tare da goya mata abinda ya faru ba.
Ga yadda ya kamata fassarar ta kasance:

Sanadi korar dalibai ba sanadin dalibai ba.

Sanadin rasa rayukan jama'a ba sanadin rayukan jama'a ba.

Sanadin hauhawar farashi ba sanadin farashi ba.

Sanadin mutuwar aure ba sanadin aure ba.

A kan haka, kenan jimlarmu za ta koma: 
"Ambaliyar ruwan ta yi sanadin hallakar karamin yaro (n) dan shekara biyar".

Da haka mai saurare zai fahimci sanadin mutuwarsa ambaliyar ruwan ta yi ba sanadin rayuwarsa ba!

Wannan tukuici ne ga mai'akatan Sashen Hausa na BBC albarkacin cikarsa shekara 65 da kafuwa.

Bashir Ahmad Zubairu (Kasarawa) Danjarida ne a Najeria

Comments

Wadanda aka fi karantawa

Iran seeks talks with us after threat of attack – Trump

U.S. President Donald Trump has said that Iranian authorities have contacted the United States to seek talks, following his threat to take military action over the killing of protesters in the country. Trump made the statement while speaking to journalists, saying that a meeting between the two sides has already been planned, but that the United States might take some action before the meeting takes place. Meanwhile, a human rights organization in Iran says it has confirmed the deaths of nearly 500 people since the outbreak of the protests. Likewise, some circulating video clips show a site outside Iran where bodies are being kept, with people going there to search for the remains of their relatives who have gone missing.

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Stepping Down Not The Right Option - Osinbajo

Vice president Yemi Osinbajo has denied reports that he intends to step down for a certain presidential aspirant ahead of the presidential primary of the All Progressives Congress (APC). The denial is contained in a statement by the chairman of Osinbajo’s campaign council, Richard Akinnola on Sunday. According to the statement, the people behind the speculation are “afraid of the huge political support base of the Vice President, Prof. Yemi Osinbajo,” adding that the VP is ready for the presidential primary scheduled to hold between June 6 and 8. The campaign council “welcomes our distinguished delegates from across the country to Abuja for our presidential primaries. “As you settle down in Abuja, we implore you to kindly disregard various fake news making the rounds that Prof. Yemi Osinbajo has stepped down. “Osinbajo would be hoping to clinch the ticket of the ruling party with much desire to take over from his principal, President Muhammadu Buhari at the end of his tenur...

An Sako Ƙarin Fasinjojin Jirgin Ƙasa Bakwai Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Wasu fasinjoji bakwai da aka yi garkuwa da su a harin jirgin kasa na ranar 28 ga Maris a jihar Kaduna sun samu 'yanci. An sako mutanen ne a safiyar Laraba bayan sun shafe kwanaki 135 a hannun ‘yan ta’addan. Sai dai ba a bayyana ko an biya kudin fansa ga 'yan ta'addar domin a sako su ba. Ɗaya daga waɗanda suka shiga sasantawar mai suna Tukur Mamu, ya fada  a wata sanarwa a ranar Laraba cewa shida daga cikin wadanda aka sako ‘yan gida daya ne, wadanda suka hada da ma’aurata da ‘ya’yansu hudu.  Sanarwar ta ce an sako yaran da iyayensu ne bayan da Sheik Ahmad Gumi ya shiga tsakani

92 Feared Dead As Oil Tanker Explodes in Sierra Leone

A huge oil tanker explodes in Sierra Leone's capital;  more than 90 people are feared dead.  Many people were injured, and most were seriously injured.  Local reports say Freetown hospitals are overcrowded.  The bomber struck shortly after noon in front of a petrol tanker.  Pictures posted on social media showed the blaze burning at the scene as the fuel spread, with several cars burning and causing an explosion.  The chairman of the National Emergency Management Agency, Lieutenant-General Brima Sesay, described the situation as "extremely serious" and said the bodies had been burnt. Bashir Ahmad Zubairu is a multi-media journalist in Nigeria Email: bashir.visionfmradio@gmail.com

We Are Not Exceptional - Zamfara State Legislators

The Zamfara state government has taken a stand against President Muhammadu Buhari's order to ban all flights across the state. State legislators voted against the move, describing it as action speaks louder than words. One of the law makers in the state who came up with the bill, Faruku Dosara, slammed the federal government and retaliated against President Buhari's security adviser, retired Major General Babagana Munguno, for his alleged negligence in the issues concerning security and prosecuting suspects involved in the case. About 300 Jangebe Science Secondary School students were recently abducted and held captive by gunmen for several days before being released, which experts say a ransom must be paid before a deal can be reached. Faruku Dosara said, "It is not only Zamfara State that has the issue of kidnapping in Nigeria, there are Dabchi, Kangara, Chibok and Kagara in Niger State. Why is Zamfara different? We are not exceptional". In a...

Why are Arab countries worried about the possible collapse of Iran’s government?

After tensions flared between Washington and Tehran following the Iranian government’s brutal crackdown on protesters, Saudi Arabia, Qatar, and Oman launched a major effort to prevent U.S. President Donald Trump from attacking Iran, out of fear that such a move would trigger a “devastating reaction in the region,” a senior Saudi official told AFP. The Saudi official said the three Gulf countries carried out intense diplomatic efforts to persuade the U.S. president to give Iran’s leaders an opportunity to show remorse, adding that communication channels remain open to help build mutual trust. How do the Persian Gulf countries view their “neighbor plagued by instability,” and what are their concerns about its current situation? Gulf diplomacy in a critical moment. The possibility of U.S. military action against Iran has been a key issue causing serious concern in Arab diplomatic efforts, especially among countries of the Gulf region. This concern stems from their proximity to...

Hukumar Hana Fasa Kwabri Ta Najeriya Ta Kama Buhunan Naman Jaki 1,339

Hukumar ta bayyana kama wannan adadin buhunan naman jaki ne a jahar Kabi da ke arewa maso yammacin Najeriya da aka kiyasta kudinsu ya haura naira miliyan 40. Shuguban hukumar ta kastam Joseph Attah ya ce sun yi nasarar kama kyafaffen naman jakin ne da aka shirya fita da shi. A cewar sa wadanda aka kama da naman sun bayyanawa hukumar cewa fiye da jakuna dubu daya suka yanka kafin su tara wannan adadi. Gwamnatin Najeriya dai ta haramta safarar jakuna zuwa kasashen ketare musamman kasar Sin, wadda ke sahun gaba wajen sayen jakuna a kasashen Afirka da suka hada da Najeriya da Nijar da Mali da Sudan da sauran su. A halin da ake ciki yanzu haka jakuna na barazanar karewa a duniya sakamakon yawan safarar su da ake tare da sarrafa nama da fatarsu ta wasu hanyoyi na daban. Hasalima dai, jaki dabba ce da kan hai fi da daya kwal a cikin shekaru ba kamar sauran dabbobi ba da ke haihuwa biyu zuwa uku a shekara.

'Yan Bindiga Sun Kai Hari Gidajen Ma'aikatan Filayen Jiragen Saman Najeria Tare Da Sace Mutum 11

Rahotanni sun ce wasu ‘yan bindiga sun kai hari a gidajen ma'aikatan Hukumar Filin Jirgin Saman Tarayyar Najeriya da ke Kaduna, inda suka yi awon gaba da akalla mutane 11. Rahotannin baya-bayan nan sun kuma bayyana cewa ‘yan bindigar sun yi nasarar sace ma’aikacin Hukumar Kula da Sararin Samaniyar Najeriya (NAMA)A, da matarsa, da jami’in Hukumar Kula da Yanayi ta Kasa (NIMET) da ya’yansa, kuma har yanzu ba a san inda suke ba. Satar mutane ya zama ruwan dare a Najeriya a yau, kuma kusan kowace safiya ana samun rahotannin kashe-kashe ko satar mutane don neman kudin fansa.  A makon da ya gabata ne shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya sha alwashin kawo karshen satar mutane a Najeriya amma ga dukkan alamu kalaman nasa ba su yi tasiri ba. 

Gunmen Killed Suswam Elder Brother

Gunmen in a car have killed Terkula Suswam, the elder brother of former Benue State Governor Gabriel Suswam. They also killed his aide in an attack that occurred at Anyiin in Gaambetiev of Logo Local Government Area at about 8.40 pm in the late evening. An eyewitness said he was working outside his compound when a Toyota car, speedily approached him. The source said the victim suspected the vehicle’s occupants to be gunmen and attempt to run into the compound before he was shot. Recent attacks and kidnapping in Nigeria lead thousand of people to leave their homes and instead end up as refugees in other places and this stuation put many in dillema.