Skip to main content

NDE Ta Zabo Matasa 1000 Don Koyar Da Su Dabarun Sana'o'i Jahar Sokoto

Hukumar samar da aikin yi ta kasa NDE, ta zabo matasa dubu daya daga Karamar Hukumar mulki ta Bodinga a Jahar Sokoto domin horas da su.

Shugabar Gudanarwar hukumar reshen jahar Sokoto Misis Eunice J. Danmallam ta bayyana cewa Hukumar NDE kamar kullum a shirye ta ke don yin hadin guiwa da gwamnatocin jahohi da kananan hukumomi da kamfunna da masana'antu kazalika da masu hannu da shuni domin tallafa al'umma a bangaren horas da su dabarun sana'o'i.
A cewa babbar jami'ar matasan da aka zabo za su koyi dabarun sana'o'i da suka hada da sana'ar walda da dunkin tela da gyaran famfo da kafintanci da hada man shafa da sauran su. Wanda wannan zai zama wani tsani da za su taka domin cimma madogara a rayuwarsu. 
A nasa jawabi, wakilin Hukumar NDE  na kasa a wurin taron Alhaji Mustapha Yakasai ya shawarci wadanda suka amfana da shiri da su dage wajen tabbatar da sun mayar da hankali wajen koyon tare da yin amfani da duka abinda suka koya domin amfanin kan su d sauran al'umma.
A nasu jawabai Sarkin Bodinga Alhaji Idris Abdul'uf da shugaban karamar Hukumar Mulki ta Bodinga wanda Alhaji Umar Magaji ya wakilta, sun nuna farin cikin su akan yadda hukumar ta NDE ta zabi Bodinga tare da bayyana cewa wannan gagarumin ci gaba ne da zai taimaka wajen rage radadin talauci a tsakanin al'umma.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Da Dumi Dumi An Ceto Yaran Da Aka Sace A Katsina

Sakataren gwamnatin jahar Katsina Alhaji Mustapha Inuwa ya fitar da sanarwar cewa an samu nasarar ceto daliban nan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su daga makarantar kwanan ta Kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina. Ya ce an ceto yaran su 340, kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta isowa jahar daga Tsafen jahar Zamfara. Ana sa ran gobe jumu'a za su gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kafin daga bisani a sada su da iyayensu. Sauran bayani zai zo nan gaba.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey