Skip to main content

NDE Ta Zabo Matasa 1000 Don Koyar Da Su Dabarun Sana'o'i Jahar Sokoto

Hukumar samar da aikin yi ta kasa NDE, ta zabo matasa dubu daya daga Karamar Hukumar mulki ta Bodinga a Jahar Sokoto domin horas da su.

Shugabar Gudanarwar hukumar reshen jahar Sokoto Misis Eunice J. Danmallam ta bayyana cewa Hukumar NDE kamar kullum a shirye ta ke don yin hadin guiwa da gwamnatocin jahohi da kananan hukumomi da kamfunna da masana'antu kazalika da masu hannu da shuni domin tallafa al'umma a bangaren horas da su dabarun sana'o'i.
A cewa babbar jami'ar matasan da aka zabo za su koyi dabarun sana'o'i da suka hada da sana'ar walda da dunkin tela da gyaran famfo da kafintanci da hada man shafa da sauran su. Wanda wannan zai zama wani tsani da za su taka domin cimma madogara a rayuwarsu. 
A nasa jawabi, wakilin Hukumar NDE  na kasa a wurin taron Alhaji Mustapha Yakasai ya shawarci wadanda suka amfana da shiri da su dage wajen tabbatar da sun mayar da hankali wajen koyon tare da yin amfani da duka abinda suka koya domin amfanin kan su d sauran al'umma.
A nasu jawabai Sarkin Bodinga Alhaji Idris Abdul'uf da shugaban karamar Hukumar Mulki ta Bodinga wanda Alhaji Umar Magaji ya wakilta, sun nuna farin cikin su akan yadda hukumar ta NDE ta zabi Bodinga tare da bayyana cewa wannan gagarumin ci gaba ne da zai taimaka wajen rage radadin talauci a tsakanin al'umma.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

WHEN LIES GO VIRAL: DEFENDING TRUTH IN NIGERIA AND WEST AFRICA’S DIGITAL PUBLIC SPHERES

Across Nigeria and West Africa, digital technology has reshaped how citizens engage with information, governance, and public debate. Mobile phones and social media platforms have become dominant sources of news, especially for young people and communities with limited access to traditional media. While this transformation has expanded civic participation and freedom of expression, it has also intensified the spread of misinformation, posing serious risks to democracy, public health, and social cohesion. Misinformation is no longer a marginal problem. It is a structural challenge that affects elections, security, development communication, and trust in public institutions. Addressing it requires coordinated action that combines ethical journalism, media literacy, platform accountability, and evidence based policy responses. THE DIGITAL INFORMATION LANDSCAPE IN NIGERIA AND WEST AFRICA Nigeria is Africa’s most populous country and one of its most digitally active societies. So...