Skip to main content

NDE Ta Zabo Matasa 1000 Don Koyar Da Su Dabarun Sana'o'i Jahar Sokoto

Hukumar samar da aikin yi ta kasa NDE, ta zabo matasa dubu daya daga Karamar Hukumar mulki ta Bodinga a Jahar Sokoto domin horas da su.

Shugabar Gudanarwar hukumar reshen jahar Sokoto Misis Eunice J. Danmallam ta bayyana cewa Hukumar NDE kamar kullum a shirye ta ke don yin hadin guiwa da gwamnatocin jahohi da kananan hukumomi da kamfunna da masana'antu kazalika da masu hannu da shuni domin tallafa al'umma a bangaren horas da su dabarun sana'o'i.
A cewa babbar jami'ar matasan da aka zabo za su koyi dabarun sana'o'i da suka hada da sana'ar walda da dunkin tela da gyaran famfo da kafintanci da hada man shafa da sauran su. Wanda wannan zai zama wani tsani da za su taka domin cimma madogara a rayuwarsu. 
A nasa jawabi, wakilin Hukumar NDE  na kasa a wurin taron Alhaji Mustapha Yakasai ya shawarci wadanda suka amfana da shiri da su dage wajen tabbatar da sun mayar da hankali wajen koyon tare da yin amfani da duka abinda suka koya domin amfanin kan su d sauran al'umma.
A nasu jawabai Sarkin Bodinga Alhaji Idris Abdul'uf da shugaban karamar Hukumar Mulki ta Bodinga wanda Alhaji Umar Magaji ya wakilta, sun nuna farin cikin su akan yadda hukumar ta NDE ta zabi Bodinga tare da bayyana cewa wannan gagarumin ci gaba ne da zai taimaka wajen rage radadin talauci a tsakanin al'umma.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

Binani Na Neman Kotu Ta Tabbatar Da Ita Wadda Ta Lashe Zaɓen Adamawa

Magoya bayan jam’iyyar PDP a jihar Adamawa a ranar Litinin sun fito kan tituna domin nuna adawa da ayyana Sanata Aishatu Dahiru Binani a matsayin wadda ta lashe zaben gwamnan Adamawa. Sai dai ita Binani ta buƙaci wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta dakatar da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta kasa (INEC) daga sauya matakin da aka ɗauka na ayyana ta da a ka yi a matsayin wadda ta lashe zaɓen.  A wata buƙata da ta shigar a ranar Litinin, mai neman izinin kotun ya nemi izinin kotun ta ba ta damar shigar da buƙatar neman umarnin haramtawa INEC daga ɗaukar duk wani mataki na watsi da sanarwar da aka yi a ranar 16 ga Afrilu da Kwamishinan zaɓen jahar, Barista Hudu Ari ya ayyana ta a matsayin wadda ta samu ƙuri'u mafifi rinjaye kuma ta lashe zaɓen alhali ba a kammala tattara sakamakon zaɓen gaba ɗaya ba. Ta kuma nemi a ba da umarnin hana hukumar zabe ta INEC, da wakilinta nadawa ko kuma duk wanda ke wakiltarta daukar wasu matakai na bayyana wanda ya lashe zaben gwamna da ak...