Skip to main content

Jirwaye Mai Kama Da Wanka - Kalaman Ahmad Gumi Da Matakin Gwamnatin Najeriya

Kalaman Dakta Ahmad Gumi da ya yi wa taken “Yaki bai taba zama mafita a ko ina” sun sabawa addini da hankali da tarihi da ma al'ada irin ta Bil Adama, domin kuwa addinin da tarihin su suka karyata su ba marubucin wannan shafin ba.  
Yana magana ne game da hare-haren da sojojin Najeriya suka kai kwanan nan kan 'yan bindiga a Zamfara da sauran jihohin arewa maso yamma, wanda ya ce ba zai kawo karshen ta'addanci ba. Ya kuma ce tattaunawa da sulhu cikin lumana da shugabannin 'yan fashin kawai za su yi, kuma a cewar sa su ne kawai mafita.

 Da farko dai, ba gaskiya ba ne cewa yaƙi bai taɓa warware wata matsala.  Domin a cikin tarihin ɗan adam, babu abin da ke warware batutuwan da ke haifar da rikice-rikice a matsayin nasara face fagen fama.  
Bari mu soma da addini, wanda shi ne jigo kafin kome ya biyo baya:
Al’ummar Musulmin farko a Madina sun sami nasarar tsira kuma a ƙarshe sun yi nasara a kan maƙiyansu na Makka saboda yawan nasarar sojoji a Badar, Uhud, Khandaq da cin Makka a shekarar 629AD. Kafiran Makka sun fitini Manzon Allah ta hanyar azabtar da musulmi da kisansu da ma bautar da su. An umurce shi da yin hijira,  wannan ba kome ba ne face matakin son zaman lafiya. Amma daga baya kafiran Makka su ka yi kokarin bin sa a can don yakarsa, da hakan ya haddasa Yakin Uhud, da musulmi suka samu nasara.
Da sun ci gaba da neman sulhu da ba a taka mu su birki ba.
Bari mu tsunduma tarihi din shi kuma, mu gani shin kalaman na Gumi gaskiya ne ko dai kawai jirwaye ne mai kama da wanka:
Tarihin duniya ya tabbatar da cewa sulhu da azzalumi ba zai taba kawo maslaha ba.
Misalai a nan da suka shafi kasashen turai na matsayin mizanin auna wannan magana. An samu nasara wajen dakatar da Napoleon Bonaparte ne kawai daga cin Turai ta hanyar samun nasarar sojoji a Rasha a shekarar 1812 da kuma a Waterloo a 1815. 
Wanda akan tilas bayan an yi masa taron dangi ya mika wuya tare da sa hannu a yarjejeniyar ya fadi, da an tsaya neman sulhu shi ma da ba hakan ba ta faru ba.
Yaƙin Duniya na Biyu, yaƙi ne mafi tsanani a tarihin ɗan Adam, ya ƙare a cikin 1945 lokacin da Axis Powers suka karɓi buƙatun Allied Powers na "mika wuya ba tare da wani sharadi ba."  Kazalika, shahararren sojan Amurkan nan Janar Douglas MacArthur ya fafata da kwamandojin Jafananawa a watan Agustan 1945 aka rinjaye shi kan tilas ya mika wuya.
Ba a kawo karshen yakin basasar Najeriya ta hanyar tattaunawa ba.  Kwamandan runduna ta 3 Kanal Obasanjo ya amince da bukatar dakarun Biafra na sun yarda su ba da kai bayan an sha wuta saboda doguwar fafatawa.  

Daga nan ya tafi da Babban Hafsan Hafsoshin Biyafara Phillip Effiong zuwa Legas don ganin Janar Gowon, inda ya karanta wani jawabi kuma ya ayyana, "Jamhuriyar Biafra ta daina wanzuwa tun daga lokacin."
Yake-yaken Basasar Amurka da Chana 1865 - 1930
Yaƙin basasar Amurka ya ƙare a cikin 1865 ba tare da tattaunawar zaman lafiya ba, bayan kwashe shekaru ana zubar da jini. Daga bisani dai a ka kawo karshensa lokacin da Babban Janar Robert E. Lee ya mika wuya ga Kwamandan Janar na Sojojin Tarayyar Ulysses Grant a Appomattox.  

Hakanan, yakin basasar China na shekarun 1930 zuwa 40 ya ƙare lokacin da Mao Zedong da tsarin Kwaminisanci suka kwace iko da birnin Beijing a 1949 kuma suka ayyana Jamhuriyar Jama'ar Kasar Sin, yayin da Marshal Chiang Kai-shek da Kuomintang suka tsere zuwa Taiwan.
 Dauki misali a baya, an warware yakin Jihadin Sokoto na 1804-08 a fagen daga. Shehu Usmanu Danfodio bai sanya hannu kan wata yarjejeniya da Sarkin Gobir ba saboda sojojin Jihadi sun kori Alkalawa kuma masarautar ta fadi. Haka ta kasance ga duk sauran masarautu a kasar Hausa.  
Mummunan yakin basasar Kano na 1893-4, ya ƙare lokacin da Yusufawa suka fatattaki askarawan Sarki Tukur gaba ɗaya, suka bi shi zuwa Katsina suka kashe shi a can, wanda ba su nemi wani sulhu ba, da a ganin su neman tattaunawa ba zai kai su samun nasara ba.  
A shekarar 1903 lokacin mulkin sarkin musulmi Attahiru Ahmadu, da sojojin Burtaniya suka kwace Sokoto, gwamnan turawan mulkin mallaka, Lord Lugard ya karanta wa Wazirin Sokoto cewa “Fulani a zamanin Danfodio sun ci kasar Hausa, su ne kuma ke mulki ba Burtaniya ba. Duk da ya ke idan an bi tarihi da kyau za a ga ba su yi sulhu da sarkin musulmi Attahiru ba, wanda kuma suka samu damar kashe shi a Burmi ta jahar Adamawa.

Wani misali mai sauki da zai nuna maka sulhu da 'yan tawaye ko 'yan ta'adda ba shi da riba shi ne yadda aka samu damar dakushe fitattun kungiyoyin 'yan tawaye a duniya.
Dubi yadda Tamil Tigers na Siri Lanka da 'yan tawayen FARC na Kolombiya da Sojojin masu turjiya na "Resistance Army" na Yuganda, RUF na Saliyo, Renamo na Mozambik,' yan tawayen Checheniya na Rasha, ETA ta Sifaniya, 'yan aware na Corsican na Faransa, Red Brigades na Italiya, Baeder-Meinhof da Red Army Japan duk an lura da yadda ta kare tsakaninsu da gwamnatocin da suke yi wa tawaye.  
A halin yanzu, yakin basasar Siriya na da shekaru goma ana fafatawa ba tare da wata yarjejeniyar zaman lafiya ba saboda Shugaba Bashar al-Assad, tare da taimakon Rasha, Iran da Hizbullah, na ci gaba da ba shi taimakon domin ya kayar da 'yan tawayen da suka dauki makami a kansa.

Wani lamari ne daban idan 'yan tawaye suka sami nasarar korar gwamnati, kamar lokacin da' yan tawaye suka kashe Mu'ammar Gaddafi a Libya ko yadda 'yan tawayen Habasha suka kori Mengistu Haile Mariam a 199, ko yadda 'yan Somaliya suka kori Shugaba Siad Barre a 1991 ko kuma kwanan nan, kungiyar Taliban da ta kori sojojin Amurka daga Afghanistan; hada da juyin mulkin soji, kamar na baya -bayan nan a Gini. 
Wanda wannan ya nuna idan har an ci gaba da neman tattaunawa da wani rikicin bai mutu ba har yanzu.

Nacewar Sheikh Gumi cewa dole ne gwamnati ta tattauna da 'yan bindigar arewa maso yamma ba daidai ba ne kuma ba zai yiwu ba.  Da farko dai, 'yan fashin ba su da wata manufa ta siyasa ko maslaha da son cibgaban al'umma sai kisa da ruguza kasa.  

Duk abin da suke da shi shine ƙaramin uzuri, cewa an mayar da su saniyar ware a Najeriya, don haka suka koma yin laifi. Sun yi kama da 'yan tawayen Janjaweed da suka tsoratar da gabashin Sudan shekaru 15 da suka gabata.
A shekarar 1992 lokacin da gwamnatin soja ta janar Ibrahim Badamasi Babangida ta yi rangwame da yawa kuma ta sanya hannu kan cikakkiyar yarjejeniya da Kungiyar Malaman Jami'a ta ASUU domin kawo karshen yajin aikin da take yi, sabon Ministan Ilimi kuma babban lauyan kundin tsarin mulki na lokacin Farfesa Ben Nwabueze ya yi watsi da yarjejeniyar cikin hanzari a watan Janairun 1993. Ya ce yarjejeniya ce “ingantacciya amma ba mai dorewa ba ”yarjejeniya ce da aka samar don gwamnati ta sasanta hakkinta na ikon raba albarkatu bisa zama da wani bangare na 'yan kasar don cimma manufa mai kyau, amma ba shi zai hanantaka birki ga mai neman wuce gona daniri ba".

Ko ta yaya, ba kamar Boko Haram ba, 'yan fashin ba su da wani shugabanci na tsakiya da gwamnati za ta iya tattaunawa da su. 
Sabanin Boko Haram, 'yan fashi ba su kokarin mamaye gwamnati da tafiyar da Najeriya.  

Manufar su ita ce su kafa dauloli da dama ba bisa ƙa'ida ba a duk faɗin yankin inda za su iya kashewa, yi wa mata fyade da sace-sace yadda suke so. 
Amurkawa suna bambanta tsakanin yaƙin "mai kyau" da "mara kyau".  Sun ce Yaƙin Duniya na Biyu da mamaye Afghanistan shine yaƙe -yaƙe masu kyau yayin da Vietnam da Iraki munanan yaƙe-yaƙe.  
Watau, idan an tilasta muku yaki kuma ba ku da wani zaɓi face kare kanku, kamar yadda 'yan fashi da Boko Haram ke yi, to wannan yaƙi ne mai kyau.  Kai hari ga wasu mutane da sunan mamaye daula ko iƙirarin ƙarya cewa suna da Makaman Kare Dangi mummunan yaƙi ne. Duka 'yan Boko Haram da' yan fashi sun kai hari kan Najeriya da al'ummarta. Fada da su da dukkan karfin da sojojin Najeriya da jami’an tsaro za su iya samu shi ne yakin da ya dace.
Idan Sojojin Najeriya, bayan tuntuɓe da yawa, yanzu sun tattara isasshen ƙarfin da za su lalata barayin, ta kowane hali ya kamata mu tallafa musu. Yakamata mu tunatar da Sojojin kawai don rage kurakurai su kuma mutunta haƙƙin ɗan adam.
Amma duuk wani mataki sabanin wannan kuskure ne.
An lura sau tari fiye da shurin masaki, sheikh Ahmad Gumi na zuwa wurin jaje da tausayawa 'yan bindiga da sunan waye musu kai da yi mu su wa'azi amma ba a taba ganin sa yana zuwa jaje a wurin wadanda farmakin 'yan bindiga ke shafa ba.
Sai dai ba mu sani ba, ko wadannan matakan da ya ke ta dauka na a kare hakkin 'yan fashin shi ne abinda ya gani cikin addini?
Wannan amsa malamai ya dace su bayar da ita.
A sani na dai adadin yawan 'yan bindiga bai kai ko kashi daya cikin dari na yawan al'ummar Najeriya ba, kan haka ina dalilin ci gaba da kare su a duk miyagun ayukansu, amma a bar jaki ana dukan taiki?

Zubairu Ahmad Bashir
Dan jarida ne kuma mai sharhi akan al'amurran yau da kullum a Najeriya.


Comments

Wadanda aka fi karantawa

National Directorate of Employment (NDE) Disburses 100,000 as a Loan to 108 Agricultural Empowerment Scheme Beneficiaries in Sokoto

The state Coordinator of the agency said this was to enable the beneficiaries to be self reliant and contribute their quota to the development of the country. She said the programme was a combined orientation made up of 108 beneficiaries of Agricultural Empowerment Scheme, Community Based Agricultural Empowerment Scheme, Sustainable Agricultural Development Empowerment Scheme and Graduate Agricultural Empowerment Scheme that were given loans of N100, 000 each. Mrs. Danmallam added that the beneficiaries are graduates of NDE agricultural Extension, Poultry and Vegetable production. She said the money disbursed to them was a loan facility which would attract a single digit simple interest rate of 9 % and will have a moratorium of six months before beneficiaries will start paying back and it is repayable in three years.  Therefore, urged the them to ensure timely repayment to enable other unemployed persons to also benefit. In his goodwill message, ...

Wata Mota Cike Da Harsasan Bindiga Ta Fada Rami A Garin Awka Na Jahar Imo

Hankalin jama'a yayi matukar tashi a jiya Lahadi biyo bayan gano wata babbar mota cike da harsasai masu rai a birnin Anacha na jahar Imo da ke kudu maso gabashin tarayyar Najeriya. Rahotannin da suka shigo muna na cewa jami'an tsaron cikin hanzari sun afkawa garin na kasuwanci domin daukar matakin gaggawa kan lamarin.  Babbar motar wadda ke dauke da kwaliyoyin harsasai masu rai ta fada cikin wani rami da ke kan titi, inda dukan harsasan suka zube. Wata majiya da ta tabbatar da faruwar lamarin ta ce: “Motar ta fadi, kuma duk titin na cike da harsasai.  Wasu yaran ma sun debi wasu da hannayensu suka gudu, kafin jami’an tsaro su iso wurin. ”  Majiyar ta ci gaba da bayyana cewa direban babbar motar da mai yi masa hidima sun yi watsi da motar bayan hatsarin ya faru, inda suka yi batan dabo zuwa inda ba a sani ba. Amma wata majiyar ta ce ‘yan sanda sun cafke direban. “Lamarin ya jawo jami'an tsaro masu yawa zuwa yankin hanyar Awka da da safiyar yau. 'Yan sanda sun...

Biden Ya Doke Trump A Georgia Da Ratar Kuri'u 12,284

 An kammala kirga kuri'un jahar Georgia da ake takaddama kan ta, in da Joe Biden ya lashe jahar da rata mai yawa. Jahar Atlanta Georgia mai yawan kuri'u miliyan biyar da doriya ta zama sha kallo a idon duniya ganin yadda shugaba Donald Trump ya yi zargin shi ne ya samu nasara a jahar kuma ya nemi sai an sake kirga dukan kurin'un da aka kada. A jiya alhamis da yamma ne aka kammala lissafin da ya kwashe kusan fiye da mako daya a na yi, in da ofishin sakataren gwamnatin jahar ya fitar da wannan sanarwa. Ofishin Brad Raffensperger ya bayyana cewa bayan sake kirga dukan kuri'un da hannu, sakamakon da aka samu tun farko yana nan bai sauya ba. Joe Biden ya doke Donald Trump da yawan kuri'u 12,284, yayin da shugaba Donald Trump ya samu 1,872.

An Ruguza Makarantar Malam Abduljabbar Kano

Dazu dazun nan gwamnatin jahar Kanon ta tura jami'an ma'aikatar lura da tsarin filaye in da ta ruguza makarantar Malam Abduljabbar. Gwamnatin dai ta taba bayyana cewa filin da ya ke amfani da shi haramtacce ne, in da ta kai ga kwace shi tare da bada umurnin gudanar da wasu muhimman ayukka a wurin. Dangantaka dai ta yi tsami tsakanin gwamnatin jahar Kano da Abduljabbar in da a ranar laraba sakataren watsa labaran gwamnatin jahar, Muhammad Garba ya bayar da sanarwar rufe masallacin Malam Abduljabbar tare da hana masa gudanar da wa'azi baki daya. In da ta ce hakan na da alaka da irin yadda ya ke tunzura jama'a a kalaman da ya ke amfani da su a lokacin da ya ke da'awa.

Gunmen Abducted 11 FAAN Staff In Kaduna

A group of gunmen yesterday attacked the residences of the Federal Airport Authority of Nigeria Kaduna. Reports say gunmen stormed the compound and abducted at least 11 people. Recent reports suggest that the bandits also abducted a staff of  Nigerian Airspace Management Agency NAMA, his wife, a National Meteorological Agency (NIMET) official and his children.Their whereabouts are still unknown. Kidnappings are common in Nigeria today, and almost every morning there are reports of killings or kidnappings for ransom. Last week Nigerian President Muhammadu Buhari vowed to end abduction in Nigeria but for all indications his words were not effective.

The Nigerian Governors Forum Describe The Militant Attack On Benue State Governor As Shocking

The Nigerian Governors Forum (NGF) has described the militant attack on the Benue State governor as "shocking" and "scary".  Governor Samuel Ortom's delegation was attacked by gunmen on Saturday on the Makurdi-Gboko road, when he visited his farm.  In a statement issued by the group's chairman and Ekiti State Governor Kayode Fayemi on Sunday, the NGF congratulated Ortom for the escape from the attack which it said was "scary and offensive".  Inspector General of Police Mohammed Adamu also condemned the attack and ordered that security be beefed up on the governor and an investigation launched.  "The NGF has said in a loud voice that efforts to rehabilitate Benue State will not succeed," the statement said.  "One of the relatives of a former governor of the state was recently killed. This kind of act of violence must be stopped for whatever reason to kill the people of Benue."

Burtaniya Ta Kakabawa Bankunan Rasha da Mahukuntan Kasar Takunkumin Tattalin Arziki Mafi Girma A Tarihi

Getty images Firaministan Burtaniya, Boris Johnson ya sanar da sakawa Rasha takunkumi mafi tsanani a bangaren tattalin arziki da Rasha ta taba gani, tun bayan da ta mamaye Ukraine. Da yake magana a zauren majalisar, firaministan ya ce za a daskarar da duk wasu manyan bankunan kasar Rasha da kuma cire su daga tsarin kudi na Burtaniya.  Har ila yau, za a dakatar da kamfanin jiragen saman Rasha na Aeroflot sauka a kasar Birtaniya. Mista Johnson ya shaidawa majalisar dokokin kasar a yammacin ranar almais din makon nan cewa, shugaban kasar Rasha Vladimir Putin "mai cin zali ne mai zubar da jini, don haka zai yabawa aya zakinta".

Yahaya Bello Ya Caccaki Buhari

Da ya ke jawabi a lokacin da ake gudanar da shirin zaben fitar da gwani, gwamnan jahar Kogi Yahaya Bello ya nemi a zabe shi domin ya magance matsalar tsaro da karancin ilmi da ake fama da su yanzu haka a Najeriya. Ya ce, "akwai takaici ace wai yanzu malaman jami'a suna ci gaba da yajin aiki, dalibai na zaune a gida kuma an kasa magance wannan matsala mai saukin magancewa". Yahaya Bello wanda ya ce ba zai jaye ma kowa a neman tikitin shugaban kasa, ya kara da cewa shi matashi ne kuma matasa ya kamata a ba dama su mulki kasar nan ba tsofaffi da suka gaji ba. Ya yabawa shugaba Buhari akan saka hannu a kan dokar ba matasa damar tsayawa takara, in da ya ce abu ne mai kyau. Ya yi kira ga mata da sauran 'yan Najeriya da ya ce ana zalunta da su zabe shi. Dan takarar ya ce "yanzu haka babu tsaro ko kadan kuma an kyale, ana kashe mutane ana kona mu su dukiya kuma ana kallo an zura ido".

Binani Ta Zama Mace Ta Farko Da AKa Zaɓa Gwamna A Najeriya

A wani abinda ba saban ba, Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta bayyana Sanata Aisha Dahiru, wacce aka fi sani da Binani a matsayin wadda ta lashe zaɓen gwamnan jahar Adamawa. Kwamishinan zaɓen jahar Adamawa, Farfesa Hudu Yunus Ari, ya ayyana Binani a matsayin wadda ta lashe zaɓen ana tsakiyar tattara sakamakon zaɓen. An bayyana sakamako daga ƙananan hukumomi 10 cikin 20 yayin da aka dage ci gaba da bayyana sakamakon zaɓen har zuwa karfe 11 na safe. Sai dai Ari ya sanar da sakamakon ƙarshe awa ɗaya kafin lokacin da aka tsara. Gwamnan jahar Ahmadu Fintiri na jam'iyyar PDP ne ke kan gaba kafin a bayyana hakan. Wasu magoya bayan jam’iyyar PDP a zauren sun nuna rashin amincewarsu da dalilin da ya sa kwamishinan zaɓe ya sanar da sakamakon maimakon baturen tattara sakamakon zaɓe a al'adance.