Skip to main content

Jirwaye Mai Kama Da Wanka - Kalaman Ahmad Gumi Da Matakin Gwamnatin Najeriya

Kalaman Dakta Ahmad Gumi da ya yi wa taken “Yaki bai taba zama mafita a ko ina” sun sabawa addini da hankali da tarihi da ma al'ada irin ta Bil Adama, domin kuwa addinin da tarihin su suka karyata su ba marubucin wannan shafin ba.  
Yana magana ne game da hare-haren da sojojin Najeriya suka kai kwanan nan kan 'yan bindiga a Zamfara da sauran jihohin arewa maso yamma, wanda ya ce ba zai kawo karshen ta'addanci ba. Ya kuma ce tattaunawa da sulhu cikin lumana da shugabannin 'yan fashin kawai za su yi, kuma a cewar sa su ne kawai mafita.

 Da farko dai, ba gaskiya ba ne cewa yaÆ™i bai taÉ“a warware wata matsala.  Domin a cikin tarihin É—an adam, babu abin da ke warware batutuwan da ke haifar da rikice-rikice a matsayin nasara face fagen fama.  
Bari mu soma da addini, wanda shi ne jigo kafin kome ya biyo baya:
Al’ummar Musulmin farko a Madina sun sami nasarar tsira kuma a Æ™arshe sun yi nasara a kan maÆ™iyansu na Makka saboda yawan nasarar sojoji a Badar, Uhud, Khandaq da cin Makka a shekarar 629AD. Kafiran Makka sun fitini Manzon Allah ta hanyar azabtar da musulmi da kisansu da ma bautar da su. An umurce shi da yin hijira,  wannan ba kome ba ne face matakin son zaman lafiya. Amma daga baya kafiran Makka su ka yi kokarin bin sa a can don yakarsa, da hakan ya haddasa Yakin Uhud, da musulmi suka samu nasara.
Da sun ci gaba da neman sulhu da ba a taka mu su birki ba.
Bari mu tsunduma tarihi din shi kuma, mu gani shin kalaman na Gumi gaskiya ne ko dai kawai jirwaye ne mai kama da wanka:
Tarihin duniya ya tabbatar da cewa sulhu da azzalumi ba zai taba kawo maslaha ba.
Misalai a nan da suka shafi kasashen turai na matsayin mizanin auna wannan magana. An samu nasara wajen dakatar da Napoleon Bonaparte ne kawai daga cin Turai ta hanyar samun nasarar sojoji a Rasha a shekarar 1812 da kuma a Waterloo a 1815. 
Wanda akan tilas bayan an yi masa taron dangi ya mika wuya tare da sa hannu a yarjejeniyar ya fadi, da an tsaya neman sulhu shi ma da ba hakan ba ta faru ba.
YaÆ™in Duniya na Biyu, yaÆ™i ne mafi tsanani a tarihin É—an Adam, ya Æ™are a cikin 1945 lokacin da Axis Powers suka karÉ“i buÆ™atun Allied Powers na "mika wuya ba tare da wani sharadi ba."  Kazalika, shahararren sojan Amurkan nan Janar Douglas MacArthur ya fafata da kwamandojin Jafananawa a watan Agustan 1945 aka rinjaye shi kan tilas ya mika wuya.
Ba a kawo karshen yakin basasar Najeriya ta hanyar tattaunawa ba.  Kwamandan runduna ta 3 Kanal Obasanjo ya amince da bukatar dakarun Biafra na sun yarda su ba da kai bayan an sha wuta saboda doguwar fafatawa.  

Daga nan ya tafi da Babban Hafsan Hafsoshin Biyafara Phillip Effiong zuwa Legas don ganin Janar Gowon, inda ya karanta wani jawabi kuma ya ayyana, "Jamhuriyar Biafra ta daina wanzuwa tun daga lokacin."
Yake-yaken Basasar Amurka da Chana 1865 - 1930
YaÆ™in basasar Amurka ya Æ™are a cikin 1865 ba tare da tattaunawar zaman lafiya ba, bayan kwashe shekaru ana zubar da jini. Daga bisani dai a ka kawo karshensa lokacin da Babban Janar Robert E. Lee ya mika wuya ga Kwamandan Janar na Sojojin Tarayyar Ulysses Grant a Appomattox.  

Hakanan, yakin basasar China na shekarun 1930 zuwa 40 ya ƙare lokacin da Mao Zedong da tsarin Kwaminisanci suka kwace iko da birnin Beijing a 1949 kuma suka ayyana Jamhuriyar Jama'ar Kasar Sin, yayin da Marshal Chiang Kai-shek da Kuomintang suka tsere zuwa Taiwan.
 Dauki misali a baya, an warware yakin Jihadin Sokoto na 1804-08 a fagen daga. Shehu Usmanu Danfodio bai sanya hannu kan wata yarjejeniya da Sarkin Gobir ba saboda sojojin Jihadi sun kori Alkalawa kuma masarautar ta fadi. Haka ta kasance ga duk sauran masarautu a kasar Hausa.  
Mummunan yakin basasar Kano na 1893-4, ya Æ™are lokacin da Yusufawa suka fatattaki askarawan Sarki Tukur gaba É—aya, suka bi shi zuwa Katsina suka kashe shi a can, wanda ba su nemi wani sulhu ba, da a ganin su neman tattaunawa ba zai kai su samun nasara ba.  
A shekarar 1903 lokacin mulkin sarkin musulmi Attahiru Ahmadu, da sojojin Burtaniya suka kwace Sokoto, gwamnan turawan mulkin mallaka, Lord Lugard ya karanta wa Wazirin Sokoto cewa “Fulani a zamanin Danfodio sun ci kasar Hausa, su ne kuma ke mulki ba Burtaniya ba. Duk da ya ke idan an bi tarihi da kyau za a ga ba su yi sulhu da sarkin musulmi Attahiru ba, wanda kuma suka samu damar kashe shi a Burmi ta jahar Adamawa.

Wani misali mai sauki da zai nuna maka sulhu da 'yan tawaye ko 'yan ta'adda ba shi da riba shi ne yadda aka samu damar dakushe fitattun kungiyoyin 'yan tawaye a duniya.
Dubi yadda Tamil Tigers na Siri Lanka da 'yan tawayen FARC na Kolombiya da Sojojin masu turjiya na "Resistance Army" na Yuganda, RUF na Saliyo, Renamo na Mozambik,' yan tawayen Checheniya na Rasha, ETA ta Sifaniya, 'yan aware na Corsican na Faransa, Red Brigades na Italiya, Baeder-Meinhof da Red Army Japan duk an lura da yadda ta kare tsakaninsu da gwamnatocin da suke yi wa tawaye.  
A halin yanzu, yakin basasar Siriya na da shekaru goma ana fafatawa ba tare da wata yarjejeniyar zaman lafiya ba saboda Shugaba Bashar al-Assad, tare da taimakon Rasha, Iran da Hizbullah, na ci gaba da ba shi taimakon domin ya kayar da 'yan tawayen da suka dauki makami a kansa.

Wani lamari ne daban idan 'yan tawaye suka sami nasarar korar gwamnati, kamar lokacin da' yan tawaye suka kashe Mu'ammar Gaddafi a Libya ko yadda 'yan tawayen Habasha suka kori Mengistu Haile Mariam a 199, ko yadda 'yan Somaliya suka kori Shugaba Siad Barre a 1991 ko kuma kwanan nan, kungiyar Taliban da ta kori sojojin Amurka daga Afghanistan; hada da juyin mulkin soji, kamar na baya -bayan nan a Gini. 
Wanda wannan ya nuna idan har an ci gaba da neman tattaunawa da wani rikicin bai mutu ba har yanzu.

Nacewar Sheikh Gumi cewa dole ne gwamnati ta tattauna da 'yan bindigar arewa maso yamma ba daidai ba ne kuma ba zai yiwu ba.  Da farko dai, 'yan fashin ba su da wata manufa ta siyasa ko maslaha da son cibgaban al'umma sai kisa da ruguza kasa.  

Duk abin da suke da shi shine ƙaramin uzuri, cewa an mayar da su saniyar ware a Najeriya, don haka suka koma yin laifi. Sun yi kama da 'yan tawayen Janjaweed da suka tsoratar da gabashin Sudan shekaru 15 da suka gabata.
A shekarar 1992 lokacin da gwamnatin soja ta janar Ibrahim Badamasi Babangida ta yi rangwame da yawa kuma ta sanya hannu kan cikakkiyar yarjejeniya da Kungiyar Malaman Jami'a ta ASUU domin kawo karshen yajin aikin da take yi, sabon Ministan Ilimi kuma babban lauyan kundin tsarin mulki na lokacin Farfesa Ben Nwabueze ya yi watsi da yarjejeniyar cikin hanzari a watan Janairun 1993. Ya ce yarjejeniya ce “ingantacciya amma ba mai dorewa ba ”yarjejeniya ce da aka samar don gwamnati ta sasanta hakkinta na ikon raba albarkatu bisa zama da wani bangare na 'yan kasar don cimma manufa mai kyau, amma ba shi zai hanantaka birki ga mai neman wuce gona daniri ba".

Ko ta yaya, ba kamar Boko Haram ba, 'yan fashin ba su da wani shugabanci na tsakiya da gwamnati za ta iya tattaunawa da su. 
Sabanin Boko Haram, 'yan fashi ba su kokarin mamaye gwamnati da tafiyar da Najeriya.  

Manufar su ita ce su kafa dauloli da dama ba bisa Æ™a'ida ba a duk faÉ—in yankin inda za su iya kashewa, yi wa mata fyade da sace-sace yadda suke so. 
Amurkawa suna bambanta tsakanin yaÆ™in "mai kyau" da "mara kyau".  Sun ce YaÆ™in Duniya na Biyu da mamaye Afghanistan shine yaÆ™e -yaÆ™e masu kyau yayin da Vietnam da Iraki munanan yaÆ™e-yaÆ™e.  
Watau, idan an tilasta muku yaki kuma ba ku da wani zaÉ“i face kare kanku, kamar yadda 'yan fashi da Boko Haram ke yi, to wannan yaÆ™i ne mai kyau.  Kai hari ga wasu mutane da sunan mamaye daula ko iÆ™irarin Æ™arya cewa suna da Makaman Kare Dangi mummunan yaÆ™i ne. Duka 'yan Boko Haram da' yan fashi sun kai hari kan Najeriya da al'ummarta. Fada da su da dukkan karfin da sojojin Najeriya da jami’an tsaro za su iya samu shi ne yakin da ya dace.
Idan Sojojin Najeriya, bayan tuntuɓe da yawa, yanzu sun tattara isasshen ƙarfin da za su lalata barayin, ta kowane hali ya kamata mu tallafa musu. Yakamata mu tunatar da Sojojin kawai don rage kurakurai su kuma mutunta haƙƙin ɗan adam.
Amma duuk wani mataki sabanin wannan kuskure ne.
An lura sau tari fiye da shurin masaki, sheikh Ahmad Gumi na zuwa wurin jaje da tausayawa 'yan bindiga da sunan waye musu kai da yi mu su wa'azi amma ba a taba ganin sa yana zuwa jaje a wurin wadanda farmakin 'yan bindiga ke shafa ba.
Sai dai ba mu sani ba, ko wadannan matakan da ya ke ta dauka na a kare hakkin 'yan fashin shi ne abinda ya gani cikin addini?
Wannan amsa malamai ya dace su bayar da ita.
A sani na dai adadin yawan 'yan bindiga bai kai ko kashi daya cikin dari na yawan al'ummar Najeriya ba, kan haka ina dalilin ci gaba da kare su a duk miyagun ayukansu, amma a bar jaki ana dukan taiki?

Zubairu Ahmad Bashir
Dan jarida ne kuma mai sharhi akan al'amurran yau da kullum a Najeriya.


Comments

Wadanda aka fi karantawa

Breaking: Chadian President Idris Deby Is Dead

  Chadian President Idris Deby died while leading the country's security forces over the weekend, fighting rebels on the northern country's border with Libya.  President Deby is widely expected to win the country's general election by 80 percent after seeking a sixth term.  The military has dissolved parliament and announced that it would hold power for 18 months before new elections.  Idris Deby took power in Chad in 1990 after overthrowing the government of former President Hissene Habry, and has ruled Chad for 30 years.

Stepping Down Not The Right Option - Osinbajo

Vice president Yemi Osinbajo has denied reports that he intends to step down for a certain presidential aspirant ahead of the presidential primary of the All Progressives Congress (APC). The denial is contained in a statement by the chairman of Osinbajo’s campaign council, Richard Akinnola on Sunday. According to the statement, the people behind the speculation are “afraid of the huge political support base of the Vice President, Prof. Yemi Osinbajo,” adding that the VP is ready for the presidential primary scheduled to hold between June 6 and 8. The campaign council “welcomes our distinguished delegates from across the country to Abuja for our presidential primaries. “As you settle down in Abuja, we implore you to kindly disregard various fake news making the rounds that Prof. Yemi Osinbajo has stepped down. “Osinbajo would be hoping to clinch the ticket of the ruling party with much desire to take over from his principal, President Muhammadu Buhari at the end of his tenur...

'Yan Bindiga Sun Kai Hari Gidajen Ma'aikatan Filayen Jiragen Saman Najeria Tare Da Sace Mutum 11

Rahotanni sun ce wasu ‘yan bindiga sun kai hari a gidajen ma'aikatan Hukumar Filin Jirgin Saman Tarayyar Najeriya da ke Kaduna, inda suka yi awon gaba da akalla mutane 11. Rahotannin baya-bayan nan sun kuma bayyana cewa ‘yan bindigar sun yi nasarar sace ma’aikacin Hukumar Kula da Sararin Samaniyar Najeriya (NAMA)A, da matarsa, da jami’in Hukumar Kula da Yanayi ta Kasa (NIMET) da ya’yansa, kuma har yanzu ba a san inda suke ba. Satar mutane ya zama ruwan dare a Najeriya a yau, kuma kusan kowace safiya ana samun rahotannin kashe-kashe ko satar mutane don neman kudin fansa.  A makon da ya gabata ne shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya sha alwashin kawo karshen satar mutane a Najeriya amma ga dukkan alamu kalaman nasa ba su yi tasiri ba. 

PDP Na Shirin Korar Wike

Gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya shigar da Æ™ara domin hana wani sabon yunÆ™urin jam’iyyar PDP dakatar da shi daga cikinta, kuma ya buÆ™aci kotun da ta É—auki mataki ga duk masu wannan aniya.  ÆŠaya daga cikin jigajigan jam'iyyar PDP da suka mayar da martani kan Æ™arar da gwamna Wike ya shigar, Mahdi Shehu, ya mayar da martani a ranar Litinin da ta gabata inda ya wallafa a shafinsa na twitter wata sanarwa cewa, “Wike ya shigar da Æ™ara kan jam’iyyar PDP mai lamba FHC/ABJ/CS/139/2023 ta hannun lauyoyinsa, DY Musa (SAN);  Douglas Moru, da C. C. Chibuike, yana neman a ba shi umarnin hana a kore shi daga PDP.”   Wike dai ya yi ta famar ruguza jam’iyyar har ma ya rasa inda za shi. Gwamnan na Ribas ya zamewa jam'iyyar PDP Æ™adangaren bakin tulu, irin yadda ya ke uwa da makarbiya tun bayan da dangantaka ta soma tsami tsakaninsa da wasu jigajigan jam'iyyar ciki kuwa har da gwamnan jahar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal.  

Farkawar Matan Afirka

Afirka nahiya ce mai dogon tarihi. Tun asali,  yawancin Turawa sun yi kokarin sanya idanu a kan nahiyar, sun ziyarce ta don neman ko dai kasuwanci, wanda a wancan lokacin wani nau'i ne na cinikin bayi ko kuma daga baya ya koma ga cinikin kayan masarufi kamar su gyada, auduga, fatun dabbobi da makamantansu. Zuwan Larabawa kuma, a wasu lardunan Afirka na lokacin, gami da yankin da ake kira "Sudaniyya", wanda ya hada da Sudan, Najeriya, Chadi, da wasu sassan Jamhuriyar Nijar, ya haifar da yaduwar Musulunci da al'adun Gabas. Daga baya, zuwan Bature ya kawo kiristanci, ilimin yamma da sauran manufofin Turawa. Nahiyar Afirka sannu a hankali tana juyawa zuwa matakai daban-daban; daga duhun kai har zuwa halin da ake ciki a yau. Ilimin addini da na zamani sun samu gindin zama a kasashen Afirka, amma har yanzu mata suna baya a wannan tafiyar. Sau da yawa za ka ga mata a yankunan karkara har ma da wasu biranen Afirka ci...

Filin Jiragen Sama Na Malam Aminu Kano Zai Ci Naira Biliyan 700

Ministan suhurin jiragen sama Alhaji Hadi Sirika, ya bayyana cewa majalisar zartaswata Æ™asa ta amince da ware fiye da naira biliyan É—ari bakwai domin aikin kwangilar gyaran filin sauka da tashin jiragen na sama na duniya na Malam Aminu Kano, wanda ya ce za kammala a cikin shekara É—aya rak. Majalisar zartaswa ta Æ™asa ta kuma amince da ware naira biliyan É—ari da goma sha bakwai domin gudanar da kwangilar gina cibiyar bincike akan man fetur ta Oloibir a yankin Naija Delta. Ministan Æ™asa a ma’aikatar albarkatun man fetur, Timipre Sylva ne ya shaidawa ‘yan jaridar fadar shugaban Æ™asa hakan, inda ya ce za a kammala aikin kwangilar a cikin shekaru biyu da rabi. Ya ce tun a 1980 gwamnatin Alhaji Shehu Aliyu Shagari ta soma aikin, amma daga bisani aka yi watsi da shi wanda a yanzu zai zama É—aya daga cikin manyan ayyukan da za a ci ga da tunawa da shugaba Muhammadu Buhari a yankin Naija Delta mai arzikin man fetur.

Dalar Amurka Na Fuskantar Barazanar Durkushewa

Shugaban kasar Brazil Luiz Inacio Lula da Silva ya soki kasar Amurka akan irin rawar da dala ke takawa a tattalin arzikin duniya tare da yin kakkausar suka ga asusun lamuni na duniya na IMF. Lula ya yi waÉ—annan kalamai a wata ziyarar aiki da ya kai Chana, jiya Alhamis a birnin Shanghai a wani bikin kaddamar da takwaransa, Dilma Rousseff a matsayin sabuwar shugabar bankin raya kasashen BRICS, da gamayyar kasashenn Brazil da Rasha da Indiya da Chana da kuma Afirka ta Kudu suka samar. "Me ya sa kowace Æ™asa za a danganta da dala don kasuwanci? Wanene ya yanke shawarar dala za ta zama kuÉ—in duniya?"  Ya Æ™ara da cewa me yasa banki kamar bankin BRICS ba zai iya samun kuÉ—in da zai gudanar da hulÉ—ar kasuwanci tsakanin Brazil da Chana ba, da ma sauran Æ™asashen duniya? Ya ce yana mamakin yadda Æ™asashe cike da rauni  su ke bin sawun amfani da dala wajen gudanar da kasuwanci alhali suna iya hakan da kuÉ—aÉ—ensu. A wata ganawa tsakanin sa da shugaban Chana Xi Jinping, da kuma ya ...

Nigerian President Vaccinated Against Covid-19

Nigerian President Muhammadu Buhari and his vice president, Professor Yemi Osinbajo, have been vaccinated with AstraZeneca vaccine, just one day after the nationwide vaccination campaign. Earlier, the Federal Government announced that as soon as the vaccine arrives in Nigeria, the President, government officials and all Governors will be at the forefront of the immunization drive which would be shown on the National Television (NTA) to set an example for other Nigerians, as well as allay their fears about the legitimacy of the vaccine. The president's doctor, Dr. Shuaibu Rafindadi, vaccinated the president at 11:53 a.m. Nigerian time (10:53 a.m. GMT) on Saturday, and Vice President Yemi Osinbajo immediately joined the process. They were also provided with electronic immunization cards by the Director General of Primary Health Care Development (NPHCDA), Dr. Faisal Shuaib. Nigeria successfully started the vaccination on Tuesday, becoming the third West African country to ...

National Directorate of Employment (NDE) Disburses 100,000 as a Loan to 108 Agricultural Empowerment Scheme Beneficiaries in Sokoto

The state Coordinator of the agency said this was to enable the beneficiaries to be self reliant and contribute their quota to the development of the country. She said the programme was a combined orientation made up of 108 beneficiaries of Agricultural Empowerment Scheme, Community Based Agricultural Empowerment Scheme, Sustainable Agricultural Development Empowerment Scheme and Graduate Agricultural Empowerment Scheme that were given loans of N100, 000 each. Mrs. Danmallam added that the beneficiaries are graduates of NDE agricultural Extension, Poultry and Vegetable production. She said the money disbursed to them was a loan facility which would attract a single digit simple interest rate of 9 % and will have a moratorium of six months before beneficiaries will start paying back and it is repayable in three years.  Therefore, urged the them to ensure timely repayment to enable other unemployed persons to also benefit. In his goodwill message, ...

Israel Targets Journalists

GAZA: An Israeli airstrike destroyed a high-rise building in Gaza City that housed offices of The Associated Press and other media outlets on Saturday, the latest step by the military to silence reporting from the territory amid its battle with the militant group Hamas. The strike came nearly an hour after the military ordered people to evacuate the building, which also housed Al-Jazeera, other offices and residential apartments. The strike brought the entire 12-story building down, collapsing with a gigantic cloud of dust. There was no immediate explanation for why it was attacked. The strike came hours after another Israeli air raid on a densely populated refugee camp in Gaza City killed at least 10 Palestinians from an extended family, mostly children, in the deadliest single strike of the current conflict. Both sides pressed for an advantage as cease-fire efforts gathered strength. The latest outburst of violence began in Jerusalem and has spread across the region, with...