Skip to main content

Za A Dakatar Da Masu Itikafi Shiga Masallatai A Bana - Sarkin Musulmi

Majalisar koli ta lamurran addinin musulunci ta Najeriya, NSCIA,  karkashin jagorancin Sarkin Musulmi Muhammad Sa'ad Abubakar III ta nemi da a hana musulmai masu shirin shiga itikaf don bautar Allah a wannan azumin Ramalana na bana, shiga kowane masallaci, sakamakon annobar korona na ci gaba da bazuwa a Najeriya.
Wannan matakin dai na zuwa ne daidai lokacin da 'yan siyasa da masu nadin sarautu ke ci gaba da gudanar da harkokinsu cikin cin koso a Najeriya.
Ko a bara ma an dauki matakai masu alaka da hakan, da sunan kandagarkin annobar Covid-19. To sai dai kwalliya ba ta biya kudin sabulu ba, kasancewar da dama daga al'umma ne suka bijerewa umurnin.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey