Skip to main content

Ta Ya Za Ku Gane Labaran Karya?

A wannan lokacin, yana da matukar wuya a gano labaran karya nan take ba tare da bincike mai zurfi ba.
Mutane na yada labarai marasa tushe a kokarin cimma wata mummunar manufa.
Misali na kwanan nan shine game da asalin Annobar Korona (Covid-19) da kuma tsarin sadarwa na intanet na 5G.
Wasu mutane kuma suna amfani da sunayen wasu shahararrun kamfanonin yada labarai wajen kaddamar da shafukansu na yanar gizon a Facebook. Za ku ga sunayen jaridu da kuka sani amma suna dauke da tambari daban-daban kuma wani lokacin ana rubuta sunayen ba bisa tsari ba.
Domin gano labaran karya a shafukan Facebook da tweeter, koyaushe a yi la'akari da abubuwan da ke ciki da tsarin harshen da aka yi amfani da shi wajen rubuta labaran. 

Wani lokaci idan asusun na bogi ne zaka ga abubuwan da ke ciki ba a tsara su ba, babu rariyar likau kuma suna cike da kurakuran nahawu.
Lura, ku tabbata kun ga alamar tabbaci mai launin shuɗi da ke nuna cewa asusun na kwarai ne kamar dai na BBC.
Ku yi nazarin labari kafin ku gaskata shi, ba kowane labari ne gaskiya ba.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

Binani Na Neman Kotu Ta Tabbatar Da Ita Wadda Ta Lashe Zaɓen Adamawa

Magoya bayan jam’iyyar PDP a jihar Adamawa a ranar Litinin sun fito kan tituna domin nuna adawa da ayyana Sanata Aishatu Dahiru Binani a matsayin wadda ta lashe zaben gwamnan Adamawa. Sai dai ita Binani ta buƙaci wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta dakatar da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta kasa (INEC) daga sauya matakin da aka ɗauka na ayyana ta da a ka yi a matsayin wadda ta lashe zaɓen.  A wata buƙata da ta shigar a ranar Litinin, mai neman izinin kotun ya nemi izinin kotun ta ba ta damar shigar da buƙatar neman umarnin haramtawa INEC daga ɗaukar duk wani mataki na watsi da sanarwar da aka yi a ranar 16 ga Afrilu da Kwamishinan zaɓen jahar, Barista Hudu Ari ya ayyana ta a matsayin wadda ta samu ƙuri'u mafifi rinjaye kuma ta lashe zaɓen alhali ba a kammala tattara sakamakon zaɓen gaba ɗaya ba. Ta kuma nemi a ba da umarnin hana hukumar zabe ta INEC, da wakilinta nadawa ko kuma duk wanda ke wakiltarta daukar wasu matakai na bayyana wanda ya lashe zaben gwamna da ak...