Skip to main content

Ba Kan Mu Aka Fara Ba - 'Yan Majalisar Zamfara

Gwamnatin jahar Zamfara ta sa kafa ta yi fatali da umurnin da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayar na hana shawagin jiragen sama a duk fadin jahar.
'Yan majalisar jahar sun yi kukan kura in da suka kada kuri'ar kin amincewa da wannan mataki da suka bayyana da ihu-bayan-hari.
Daya daga mahunkuntan da ya fito da kudirin har ya samu amincewa, Faruku Dosara yayi terere wa gwamnatin tarayya tare da raddi ga mai ba shugaba Buhari shawara kan lamurran tsaro, Manjo Janar Babagana Munguno mai ritaya, dangane da sakaci da ya zarge shi da yi kan lamurran da suka shafi tsaro da hukunta wadanda ake zargi da hannu ga sha'anin.
Kwanan nan dai ne aka yi garkuwa da daliban makarantar Sakandiren Kimiyya ta Jangebe su kimanin 300 da suka shafe kwanaki a hannun 'yan bindiga kafin sakin su, abinda masana ke zargin sai da aka biya kudin fansa kafin a cimma yarjejeniyar, lamarin da zai iya ci gaba da dagula matsalar tsaro a Najeriya.
Faruku Dosara ya ce, "ai ba jahar Zamfara kadai aka soma satar jama'a a Najeriya ba, akwai Dabchi da Kangara da Chibok ga kuma Kagara a jahar Naija, me zai sa Zamfara ta zama ta daban, to ba kan mu aka fara ba".
Ko baya ga satar mutane don neman kudin fansa hare-haren da 'yan bindigar ke kaiwa ya jawo hallakar daruruwan rayukan jama'a a jahar.
Wannan turka-turka da ta kunno kai ba a san in da za ta tsaya ba. Kwanan nan ma an jiyo gwamnan jahar Bello Mutawalle na cewa ba ya nesa ga fasa kwai don fallasa masu hannu a kashe-kashe da jerin hare-haren da ake kaiwa jahar ta Zamfara.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

Gwamnatin Najeriya Ta Shirya Da ASUU

 An kai matsaya tsakanin Kungiyar Malaman Jami'o'i ASUU in da gwamnatin tarayya ta amince da bukatunsu. A jiya jumu'a dai ne suka yi wani zama don ganin malaman sun janye yajin aikin da ya dauki watanni bakwai ana yi. A yanzu dai gwamntin Najeriya ta amince da cire malaman daga tsarin albashi na IPPIS wanda suka jima suna turjiya akai, kuma za ta biya malaman albashin duk watannin da su ke bi. Haka ma ministan kwadagon Najeriya Cris Ngige ya tabbatarwa manema labarai cewa, za a karawa malaman jami'ar alwus da zai kai naira biliyan 35 sabanin yadda yake a da na biliyan 30. Ngige ya kuma ce za a ci gaba da tattaunawa kan sabon tsarin albashi na UTAS muddin an kammala tsara shi. A nasu bangare kungiyar malaman jami'o'in sun yi maraba da wannan yunkuri, in da ake ganin matakin ga alama zai iya kawo karshen dogon yajin aikin da aka dade ana yi.

Me Ku Ka Sani Game Da Labari Maras Daɗi (Negative Story)?

Galibin wasu mutane na ganin 'yan jarida ba su cika bayar da labarai ma su daɗi ba face waɗanda suka shafi tashin hankali da tonon silili da ƙwanƙwanto da kuma na haɗurra. Wannan fahimta kuwa na da nasaba da kasa fahimtar aikin jaridar kansa da wanda ke yin sa. Ni a ganina duk wani labari da ya shafi ayyukan muggan mutane da ya munanawa mutane na gari shi zan mayarwa hankali domin fallasa mai mugunta da farantawa wanda aka zalunta. Bari mu soma da mai sauƙi kafin mu duba ma su sarkakiya. Idan haɗari ya faru, misali na mota ko jirgin sama ko na kasa ko kuma gobara ko ambaliyar ruwa; za mu bayar da labarin. Shin ka san ba muna bayar da labarin ne saboda kawai a ji an mutu ko an kaririye ko an yi hasarar dukiya ba? GA AMSA:  Game da haɗari ko gobara da sauran iftila'i mu kan bayar da wannan labari saboda bayyana halin waɗanda matsalar ta rutsa da su, domin samun agajin hukumomi da masu iya tallafawa. Mu kan bayar da labarin saboda jawo hankalin hukumomin tsaro da saura...