Skip to main content

An Yabi Babban Bankin Najeriya (CBN) Kan Fito Da Tsarin Bani Naira In Ba Ka Dala

Shugabar Hukumar kula da 'yan Najeriya mazauna kasashen waje (NIDCOM) Abike Dabiri-Erewa, ta yaba wa Babban Bankin Najeriya (CBN) kan bullo da shirin.
A wata sanarwa da jami'in hulda da jama’a na NIDCOM, Abdur-Rahman Balogun ya sanya wa hannu, Dabiri-Erewa ta ce shirin wani abin ci gaba ne da aka yi maraba da shi, domin zai karfafawa maziyarta damar aika kudi ta hanyoyin hukuma.

Shi ma bankin na CBN, ya bayyana cewa wannan tsari wani kwarin gwiwa da ci gaba ne ga masu musayar kudaden kasashen waje inda masu aiko da kudaden zasu biya naira 5 a kan kowace dala da aka ka shigo da ita.
 Dabirewa ta ce manufar idan aka aiwatar da ita yadda ya kamata, za ta yi tasiri ga tattalin arzikin Najeriya.

Ta ce yanzu haka ofishin hulda da 'yan Najeriya mazauna kasashen wajen na kan samar da wani asusun na musamman ta yadda ‘yan Nijeriya mazauna kasashen wajen za su iya tsarawa da kuma gabatar da jarin su, da sauran lamurran da suka shafi hada-hadar kudi.

Babban bankin na CBN ya yi bayanin cewa ana sa ran wannan sabuwar manufar za ta jawo hankulan mazuna kasashen ketare ta hanyar sanya kudadensu a inda ya dace, zai kuma yi matukar tallafawa tattalin arzikin Najeriya.


Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Da Dumi Dumi An Ceto Yaran Da Aka Sace A Katsina

Sakataren gwamnatin jahar Katsina Alhaji Mustapha Inuwa ya fitar da sanarwar cewa an samu nasarar ceto daliban nan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su daga makarantar kwanan ta Kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina. Ya ce an ceto yaran su 340, kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta isowa jahar daga Tsafen jahar Zamfara. Ana sa ran gobe jumu'a za su gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kafin daga bisani a sada su da iyayensu. Sauran bayani zai zo nan gaba.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey