Skip to main content

An Yabi Babban Bankin Najeriya (CBN) Kan Fito Da Tsarin Bani Naira In Ba Ka Dala

Shugabar Hukumar kula da 'yan Najeriya mazauna kasashen waje (NIDCOM) Abike Dabiri-Erewa, ta yaba wa Babban Bankin Najeriya (CBN) kan bullo da shirin.
A wata sanarwa da jami'in hulda da jama’a na NIDCOM, Abdur-Rahman Balogun ya sanya wa hannu, Dabiri-Erewa ta ce shirin wani abin ci gaba ne da aka yi maraba da shi, domin zai karfafawa maziyarta damar aika kudi ta hanyoyin hukuma.

Shi ma bankin na CBN, ya bayyana cewa wannan tsari wani kwarin gwiwa da ci gaba ne ga masu musayar kudaden kasashen waje inda masu aiko da kudaden zasu biya naira 5 a kan kowace dala da aka ka shigo da ita.
 Dabirewa ta ce manufar idan aka aiwatar da ita yadda ya kamata, za ta yi tasiri ga tattalin arzikin Najeriya.

Ta ce yanzu haka ofishin hulda da 'yan Najeriya mazauna kasashen wajen na kan samar da wani asusun na musamman ta yadda ‘yan Nijeriya mazauna kasashen wajen za su iya tsarawa da kuma gabatar da jarin su, da sauran lamurran da suka shafi hada-hadar kudi.

Babban bankin na CBN ya yi bayanin cewa ana sa ran wannan sabuwar manufar za ta jawo hankulan mazuna kasashen ketare ta hanyar sanya kudadensu a inda ya dace, zai kuma yi matukar tallafawa tattalin arzikin Najeriya.


Comments

Popular posts from this blog

Iran seeks talks with us after threat of attack – Trump

U.S. President Donald Trump has said that Iranian authorities have contacted the United States to seek talks, following his threat to take military action over the killing of protesters in the country. Trump made the statement while speaking to journalists, saying that a meeting between the two sides has already been planned, but that the United States might take some action before the meeting takes place. Meanwhile, a human rights organization in Iran says it has confirmed the deaths of nearly 500 people since the outbreak of the protests. Likewise, some circulating video clips show a site outside Iran where bodies are being kept, with people going there to search for the remains of their relatives who have gone missing.

WHEN LIES GO VIRAL: DEFENDING TRUTH IN NIGERIA AND WEST AFRICA’S DIGITAL PUBLIC SPHERES

Across Nigeria and West Africa, digital technology has reshaped how citizens engage with information, governance, and public debate. Mobile phones and social media platforms have become dominant sources of news, especially for young people and communities with limited access to traditional media. While this transformation has expanded civic participation and freedom of expression, it has also intensified the spread of misinformation, posing serious risks to democracy, public health, and social cohesion. Misinformation is no longer a marginal problem. It is a structural challenge that affects elections, security, development communication, and trust in public institutions. Addressing it requires coordinated action that combines ethical journalism, media literacy, platform accountability, and evidence based policy responses. THE DIGITAL INFORMATION LANDSCAPE IN NIGERIA AND WEST AFRICA Nigeria is Africa’s most populous country and one of its most digitally active societies. So...

Turai na fuskantar tsananin zafi

Burtaniya  Wani matsanancin yanayin zafi ya karaɗe yammaci da arewacin Turai, inda yanayin zafi ya zarta yadda aka saba sosai, kuma ya kai yanayin da aka jima ba a gani irinsa ba a ƙasasahe da dama. Birtaniya da Faransa sun fuskanci yanayin zafin da ba su taɓa ganin irinsa ba a watan Mayu, yayin da iska mai huci ta sa zafin ya kai ƙoluwar da ba a saba ganin irinsa ba ko da a lokacin tsanananin zafi.  Paris a Faransa  Jami’an kula da yanayi sun yi gargaɗin cewa yanayin zafin wata alama ce ta ɗumamar duniya.