Skip to main content

An Yabi Babban Bankin Najeriya (CBN) Kan Fito Da Tsarin Bani Naira In Ba Ka Dala

Shugabar Hukumar kula da 'yan Najeriya mazauna kasashen waje (NIDCOM) Abike Dabiri-Erewa, ta yaba wa Babban Bankin Najeriya (CBN) kan bullo da shirin.
A wata sanarwa da jami'in hulda da jama’a na NIDCOM, Abdur-Rahman Balogun ya sanya wa hannu, Dabiri-Erewa ta ce shirin wani abin ci gaba ne da aka yi maraba da shi, domin zai karfafawa maziyarta damar aika kudi ta hanyoyin hukuma.

Shi ma bankin na CBN, ya bayyana cewa wannan tsari wani kwarin gwiwa da ci gaba ne ga masu musayar kudaden kasashen waje inda masu aiko da kudaden zasu biya naira 5 a kan kowace dala da aka ka shigo da ita.
 Dabirewa ta ce manufar idan aka aiwatar da ita yadda ya kamata, za ta yi tasiri ga tattalin arzikin Najeriya.

Ta ce yanzu haka ofishin hulda da 'yan Najeriya mazauna kasashen wajen na kan samar da wani asusun na musamman ta yadda ‘yan Nijeriya mazauna kasashen wajen za su iya tsarawa da kuma gabatar da jarin su, da sauran lamurran da suka shafi hada-hadar kudi.

Babban bankin na CBN ya yi bayanin cewa ana sa ran wannan sabuwar manufar za ta jawo hankulan mazuna kasashen ketare ta hanyar sanya kudadensu a inda ya dace, zai kuma yi matukar tallafawa tattalin arzikin Najeriya.


Comments

Wadanda aka fi karantawa

Gwamnatin Najeriya Ta Shirya Da ASUU

 An kai matsaya tsakanin Kungiyar Malaman Jami'o'i ASUU in da gwamnatin tarayya ta amince da bukatunsu. A jiya jumu'a dai ne suka yi wani zama don ganin malaman sun janye yajin aikin da ya dauki watanni bakwai ana yi. A yanzu dai gwamntin Najeriya ta amince da cire malaman daga tsarin albashi na IPPIS wanda suka jima suna turjiya akai, kuma za ta biya malaman albashin duk watannin da su ke bi. Haka ma ministan kwadagon Najeriya Cris Ngige ya tabbatarwa manema labarai cewa, za a karawa malaman jami'ar alwus da zai kai naira biliyan 35 sabanin yadda yake a da na biliyan 30. Ngige ya kuma ce za a ci gaba da tattaunawa kan sabon tsarin albashi na UTAS muddin an kammala tsara shi. A nasu bangare kungiyar malaman jami'o'in sun yi maraba da wannan yunkuri, in da ake ganin matakin ga alama zai iya kawo karshen dogon yajin aikin da aka dade ana yi.

Me Ku Ka Sani Game Da Labari Maras Daɗi (Negative Story)?

Galibin wasu mutane na ganin 'yan jarida ba su cika bayar da labarai ma su daɗi ba face waɗanda suka shafi tashin hankali da tonon silili da ƙwanƙwanto da kuma na haɗurra. Wannan fahimta kuwa na da nasaba da kasa fahimtar aikin jaridar kansa da wanda ke yin sa. Ni a ganina duk wani labari da ya shafi ayyukan muggan mutane da ya munanawa mutane na gari shi zan mayarwa hankali domin fallasa mai mugunta da farantawa wanda aka zalunta. Bari mu soma da mai sauƙi kafin mu duba ma su sarkakiya. Idan haɗari ya faru, misali na mota ko jirgin sama ko na kasa ko kuma gobara ko ambaliyar ruwa; za mu bayar da labarin. Shin ka san ba muna bayar da labarin ne saboda kawai a ji an mutu ko an kaririye ko an yi hasarar dukiya ba? GA AMSA:  Game da haɗari ko gobara da sauran iftila'i mu kan bayar da wannan labari saboda bayyana halin waɗanda matsalar ta rutsa da su, domin samun agajin hukumomi da masu iya tallafawa. Mu kan bayar da labarin saboda jawo hankalin hukumomin tsaro da saura...