Skip to main content

An Dakile Yunkurin Juyin Mulki A Nijar

Kwanaki biyu rak suka rage a rantsar da sabuwar gwamnati a Jamhuriyar Nijar wasu sojoji suka yi wani yunkurin juyin mulki a daren jiya talata.
Rahotanni da ke shigowa yanzu haka na cewa tun da misalin karfe 3:00 na daren jiya ne aka soma jiyo harbe-haben bindiga a fadar gwamnatin kasar.
Sai dai kamfanin dilancin labaru na AFP ya ruwaito cewa an dakile matakin.
A yau birnin Yamai ya zama cikin shirin ko-ta-kwana. Kawo yanzu dai babu wani cikakken bayani game da manufar wannan sabon yunkurin juyin mulkin da ma wadanda suka so kaddamar da shi.
Kasar Nijar dai ta dade tana fuskantar yawan juyin mulki tun daga lokacin sojoji ya zuwa yau. In da da dama daga shugabannin kasar da suka hada da Saleh Kumchey, Baare Mainasara har kawo Mammadou Tandja ake samun juyin mulkin sojoji.
Bayan kammala zaben shugaban kasa da ya gudana a ranar 28 ga watan Febrairun da ya gabata, wanda Bazoum Mohammed yayi nasara akan Mohammed Ousmane, ake sa ran a karon farko za a mika mulki daga wata gwamnatin farar hula zuwa wata.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

WHEN LIES GO VIRAL: DEFENDING TRUTH IN NIGERIA AND WEST AFRICA’S DIGITAL PUBLIC SPHERES

Across Nigeria and West Africa, digital technology has reshaped how citizens engage with information, governance, and public debate. Mobile phones and social media platforms have become dominant sources of news, especially for young people and communities with limited access to traditional media. While this transformation has expanded civic participation and freedom of expression, it has also intensified the spread of misinformation, posing serious risks to democracy, public health, and social cohesion. Misinformation is no longer a marginal problem. It is a structural challenge that affects elections, security, development communication, and trust in public institutions. Addressing it requires coordinated action that combines ethical journalism, media literacy, platform accountability, and evidence based policy responses. THE DIGITAL INFORMATION LANDSCAPE IN NIGERIA AND WEST AFRICA Nigeria is Africa’s most populous country and one of its most digitally active societies. So...