Skip to main content

An Dakile Yunkurin Juyin Mulki A Nijar

Kwanaki biyu rak suka rage a rantsar da sabuwar gwamnati a Jamhuriyar Nijar wasu sojoji suka yi wani yunkurin juyin mulki a daren jiya talata.
Rahotanni da ke shigowa yanzu haka na cewa tun da misalin karfe 3:00 na daren jiya ne aka soma jiyo harbe-haben bindiga a fadar gwamnatin kasar.
Sai dai kamfanin dilancin labaru na AFP ya ruwaito cewa an dakile matakin.
A yau birnin Yamai ya zama cikin shirin ko-ta-kwana. Kawo yanzu dai babu wani cikakken bayani game da manufar wannan sabon yunkurin juyin mulkin da ma wadanda suka so kaddamar da shi.
Kasar Nijar dai ta dade tana fuskantar yawan juyin mulki tun daga lokacin sojoji ya zuwa yau. In da da dama daga shugabannin kasar da suka hada da Saleh Kumchey, Baare Mainasara har kawo Mammadou Tandja ake samun juyin mulkin sojoji.
Bayan kammala zaben shugaban kasa da ya gudana a ranar 28 ga watan Febrairun da ya gabata, wanda Bazoum Mohammed yayi nasara akan Mohammed Ousmane, ake sa ran a karon farko za a mika mulki daga wata gwamnatin farar hula zuwa wata.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

Gwamnatin Najeriya Ta Shirya Da ASUU

 An kai matsaya tsakanin Kungiyar Malaman Jami'o'i ASUU in da gwamnatin tarayya ta amince da bukatunsu. A jiya jumu'a dai ne suka yi wani zama don ganin malaman sun janye yajin aikin da ya dauki watanni bakwai ana yi. A yanzu dai gwamntin Najeriya ta amince da cire malaman daga tsarin albashi na IPPIS wanda suka jima suna turjiya akai, kuma za ta biya malaman albashin duk watannin da su ke bi. Haka ma ministan kwadagon Najeriya Cris Ngige ya tabbatarwa manema labarai cewa, za a karawa malaman jami'ar alwus da zai kai naira biliyan 35 sabanin yadda yake a da na biliyan 30. Ngige ya kuma ce za a ci gaba da tattaunawa kan sabon tsarin albashi na UTAS muddin an kammala tsara shi. A nasu bangare kungiyar malaman jami'o'in sun yi maraba da wannan yunkuri, in da ake ganin matakin ga alama zai iya kawo karshen dogon yajin aikin da aka dade ana yi.

Me Ku Ka Sani Game Da Labari Maras Daɗi (Negative Story)?

Galibin wasu mutane na ganin 'yan jarida ba su cika bayar da labarai ma su daɗi ba face waɗanda suka shafi tashin hankali da tonon silili da ƙwanƙwanto da kuma na haɗurra. Wannan fahimta kuwa na da nasaba da kasa fahimtar aikin jaridar kansa da wanda ke yin sa. Ni a ganina duk wani labari da ya shafi ayyukan muggan mutane da ya munanawa mutane na gari shi zan mayarwa hankali domin fallasa mai mugunta da farantawa wanda aka zalunta. Bari mu soma da mai sauƙi kafin mu duba ma su sarkakiya. Idan haɗari ya faru, misali na mota ko jirgin sama ko na kasa ko kuma gobara ko ambaliyar ruwa; za mu bayar da labarin. Shin ka san ba muna bayar da labarin ne saboda kawai a ji an mutu ko an kaririye ko an yi hasarar dukiya ba? GA AMSA:  Game da haɗari ko gobara da sauran iftila'i mu kan bayar da wannan labari saboda bayyana halin waɗanda matsalar ta rutsa da su, domin samun agajin hukumomi da masu iya tallafawa. Mu kan bayar da labarin saboda jawo hankalin hukumomin tsaro da saura...