Skip to main content

An Dakile Yunkurin Juyin Mulki A Nijar

Kwanaki biyu rak suka rage a rantsar da sabuwar gwamnati a Jamhuriyar Nijar wasu sojoji suka yi wani yunkurin juyin mulki a daren jiya talata.
Rahotanni da ke shigowa yanzu haka na cewa tun da misalin karfe 3:00 na daren jiya ne aka soma jiyo harbe-haben bindiga a fadar gwamnatin kasar.
Sai dai kamfanin dilancin labaru na AFP ya ruwaito cewa an dakile matakin.
A yau birnin Yamai ya zama cikin shirin ko-ta-kwana. Kawo yanzu dai babu wani cikakken bayani game da manufar wannan sabon yunkurin juyin mulkin da ma wadanda suka so kaddamar da shi.
Kasar Nijar dai ta dade tana fuskantar yawan juyin mulki tun daga lokacin sojoji ya zuwa yau. In da da dama daga shugabannin kasar da suka hada da Saleh Kumchey, Baare Mainasara har kawo Mammadou Tandja ake samun juyin mulkin sojoji.
Bayan kammala zaben shugaban kasa da ya gudana a ranar 28 ga watan Febrairun da ya gabata, wanda Bazoum Mohammed yayi nasara akan Mohammed Ousmane, ake sa ran a karon farko za a mika mulki daga wata gwamnatin farar hula zuwa wata.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey